• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Ƙaddamar Da Hukumar Gudanarwar Asusun Kula Da Baƙin Haure

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
NIS

A wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa yaƙi da safarar baƙin haure, Hukumar Kula da Shige da Fice ta ƙasa (NIS) ta ƙaddamar da hukumar kula da asusun kula da ayyukan fasa ƙwaurin baƙin haure a hedikwatarta da ke Abuja.

  • Tikitin Tinubu Da Shettima: Yadda Tarihi Ya Maimaita Kansa

ƙaddamarwar tana nuna wani gagarumin ci gaba a ƙudurin da NIS take da shi na ba wai kawai yaƙi da mutanen da ke yin safarar baƙin haure ba har ma da tabbatar da cewa waɗanda aka ceto daga masu safarar baƙin hauren an kula da su don ci gaba da rayuwarsu.

NIS
Shugaban NIS, CGI Isah Jere Idris tare da wakilin Ministan Cikin Gida, Mista Peter Obodo

Da yake jawabi jim kaɗan bayan ƙaddamar da hukumar, Ministan harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola wanda wani Darakta a ma’aikatar Cikin Gida, Mista Peter Obodo ya wakilta, ya yaba wa hukumar bisa kafa wannan asusun tare da yin kira ga mambobin kula da asusun su tashi tsaye wajen yaƙi da ayyukan masu fasa ƙwaurin baƙin haure.

NIS
Yayin ƙaddamar da Hukumar Kula da Asusun

Ya nunar da cewa daga yanzu, masu safarar baƙin haure ba za su ci gaba da cin karensu ba babbaka ba kamar yadda suka saba.

Tun da farko a nasa jawabin, Shugaban NIS, CGI Isah Jere Idris wanda shi ne shugaban hukumar kula da asusun, ya bayyana cewa ‘ayyukan masu safarar baƙin haure sun ɗauki wani sabon salo da ba za a taɓa amincewa da su ba, don haka ya kamata a yi duk mai yiwuwa wajen ganin an magance.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

“Taron da muke yi a yau yana ɗaya daga cikin irin ƙoƙarin da muke yi na ganin mun yi wani ƙwaƙƙwaran bayani game da shirye-shiryen da muke yi na ganin masu fasa ƙwaurin baƙin haure sun kwashi kashinsu a hannu.” In ji shi.

Ya sake nanata cewa aikin hukumar asusun yana da tsauri kuma da girma don haka yana buƙatar dogon lokaci, jajircewa da gogewa daga membobin don samun nasara mai kyau a yaƙi da safarar baƙin haure.

NIS
Jami’an NIS a wurin taron

Sashe na 97 na Dokar Shige da Fice ta 2015 ya tanadi kafa Asusun Tallafa Wa Baƙin Haure wanda zai riƙa samun kuɗaɗen gudanarwa daga duk abin da aka samu na dukiya da sayar da kadarorin masu safarar baƙin hauren bisa sahalewar kotu.

Har ila yau, ya tanadi cewa Hukumar Gudanarwa na Asusun za ta ƙunshi wakilai daga: Ma’aikatar Cikin Gida; Kwanturola Janar na Hukumar Shige da Fice (NIS) a matsayin shugaba; Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya; Ma’aikatar Kudi ta Tarayya; Ma’aikatar Harkokin Mata da Ci gaban Al’umma ta Tarayya da Ofishin Akanta-Janar.
Sauran sun haɗa da: Ofishin Babban Mai Binciken Kuɗi; Babban Bankin Nijeriya; da kuma Hukumar Hana Fataucin Bil’adama ta ƙasa (NAPTIP) da sauransu.

Cikin manyan abubuwan da aka gudanar a taron akwai ƙaddamar da wakilan asusun daga ma’aikatu da hukumomin da suka haɗa da: Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, da ta Harkokin Mata da Ci gaban Jama’a, da NAPTIP, da Ofishin Akanta-Janar da sauran wadanda Mista Peter Obodo mai wakiltar ma’aikatar cikin gida ya gabatar.

Ƙaddamar da Hukumar Gudanarwar Asusun dai, na nuna an sake ayyana yaƙi da masu safarar baƙin haure da haramtattun kadarorinsu cikin sabon salo da zai zama mai alfanu a bisa jagorancin shugaban hukumar ta NIS, CGI Isah Jere Idris.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump
Manyan Labarai

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

November 10, 2025
Next Post
Farashin Alkama Ya Sauka a Duniya

Farashin Alkama Ya Sauka a Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

November 10, 2025
Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

November 10, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo

November 10, 2025
FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.