ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Ƙaddamar Da Hukumar Gudanarwar Asusun Kula Da Baƙin Haure

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
NIS

A wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa yaƙi da safarar baƙin haure, Hukumar Kula da Shige da Fice ta ƙasa (NIS) ta ƙaddamar da hukumar kula da asusun kula da ayyukan fasa ƙwaurin baƙin haure a hedikwatarta da ke Abuja.

  • Tikitin Tinubu Da Shettima: Yadda Tarihi Ya Maimaita Kansa

ƙaddamarwar tana nuna wani gagarumin ci gaba a ƙudurin da NIS take da shi na ba wai kawai yaƙi da mutanen da ke yin safarar baƙin haure ba har ma da tabbatar da cewa waɗanda aka ceto daga masu safarar baƙin hauren an kula da su don ci gaba da rayuwarsu.

NIS
Shugaban NIS, CGI Isah Jere Idris tare da wakilin Ministan Cikin Gida, Mista Peter Obodo

Da yake jawabi jim kaɗan bayan ƙaddamar da hukumar, Ministan harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola wanda wani Darakta a ma’aikatar Cikin Gida, Mista Peter Obodo ya wakilta, ya yaba wa hukumar bisa kafa wannan asusun tare da yin kira ga mambobin kula da asusun su tashi tsaye wajen yaƙi da ayyukan masu fasa ƙwaurin baƙin haure.

ADVERTISEMENT
NIS
Yayin ƙaddamar da Hukumar Kula da Asusun

Ya nunar da cewa daga yanzu, masu safarar baƙin haure ba za su ci gaba da cin karensu ba babbaka ba kamar yadda suka saba.

Tun da farko a nasa jawabin, Shugaban NIS, CGI Isah Jere Idris wanda shi ne shugaban hukumar kula da asusun, ya bayyana cewa ‘ayyukan masu safarar baƙin haure sun ɗauki wani sabon salo da ba za a taɓa amincewa da su ba, don haka ya kamata a yi duk mai yiwuwa wajen ganin an magance.

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

“Taron da muke yi a yau yana ɗaya daga cikin irin ƙoƙarin da muke yi na ganin mun yi wani ƙwaƙƙwaran bayani game da shirye-shiryen da muke yi na ganin masu fasa ƙwaurin baƙin haure sun kwashi kashinsu a hannu.” In ji shi.

Ya sake nanata cewa aikin hukumar asusun yana da tsauri kuma da girma don haka yana buƙatar dogon lokaci, jajircewa da gogewa daga membobin don samun nasara mai kyau a yaƙi da safarar baƙin haure.

NIS
Jami’an NIS a wurin taron

Sashe na 97 na Dokar Shige da Fice ta 2015 ya tanadi kafa Asusun Tallafa Wa Baƙin Haure wanda zai riƙa samun kuɗaɗen gudanarwa daga duk abin da aka samu na dukiya da sayar da kadarorin masu safarar baƙin hauren bisa sahalewar kotu.

Har ila yau, ya tanadi cewa Hukumar Gudanarwa na Asusun za ta ƙunshi wakilai daga: Ma’aikatar Cikin Gida; Kwanturola Janar na Hukumar Shige da Fice (NIS) a matsayin shugaba; Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya; Ma’aikatar Kudi ta Tarayya; Ma’aikatar Harkokin Mata da Ci gaban Al’umma ta Tarayya da Ofishin Akanta-Janar.
Sauran sun haɗa da: Ofishin Babban Mai Binciken Kuɗi; Babban Bankin Nijeriya; da kuma Hukumar Hana Fataucin Bil’adama ta ƙasa (NAPTIP) da sauransu.

Cikin manyan abubuwan da aka gudanar a taron akwai ƙaddamar da wakilan asusun daga ma’aikatu da hukumomin da suka haɗa da: Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, da ta Harkokin Mata da Ci gaban Jama’a, da NAPTIP, da Ofishin Akanta-Janar da sauran wadanda Mista Peter Obodo mai wakiltar ma’aikatar cikin gida ya gabatar.

Ƙaddamar da Hukumar Gudanarwar Asusun dai, na nuna an sake ayyana yaƙi da masu safarar baƙin haure da haramtattun kadarorinsu cikin sabon salo da zai zama mai alfanu a bisa jagorancin shugaban hukumar ta NIS, CGI Isah Jere Idris.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama
Manyan Labarai

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya
Labarai

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola
Manyan Labarai

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Next Post
Farashin Alkama Ya Sauka a Duniya

Farashin Alkama Ya Sauka a Duniya

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.