ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Ƙaddamar Da Hukumar Gudanarwar Asusun Kula Da Baƙin Haure

by Abdulrazaq Yahuza
4 years ago
NIS

A wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa yaƙi da safarar baƙin haure, Hukumar Kula da Shige da Fice ta ƙasa (NIS) ta ƙaddamar da hukumar kula da asusun kula da ayyukan fasa ƙwaurin baƙin haure a hedikwatarta da ke Abuja.

  • Tikitin Tinubu Da Shettima: Yadda Tarihi Ya Maimaita Kansa

ƙaddamarwar tana nuna wani gagarumin ci gaba a ƙudurin da NIS take da shi na ba wai kawai yaƙi da mutanen da ke yin safarar baƙin haure ba har ma da tabbatar da cewa waɗanda aka ceto daga masu safarar baƙin hauren an kula da su don ci gaba da rayuwarsu.

NIS
Shugaban NIS, CGI Isah Jere Idris tare da wakilin Ministan Cikin Gida, Mista Peter Obodo

Da yake jawabi jim kaɗan bayan ƙaddamar da hukumar, Ministan harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola wanda wani Darakta a ma’aikatar Cikin Gida, Mista Peter Obodo ya wakilta, ya yaba wa hukumar bisa kafa wannan asusun tare da yin kira ga mambobin kula da asusun su tashi tsaye wajen yaƙi da ayyukan masu fasa ƙwaurin baƙin haure.

ADVERTISEMENT
NIS
Yayin ƙaddamar da Hukumar Kula da Asusun

Ya nunar da cewa daga yanzu, masu safarar baƙin haure ba za su ci gaba da cin karensu ba babbaka ba kamar yadda suka saba.

Tun da farko a nasa jawabin, Shugaban NIS, CGI Isah Jere Idris wanda shi ne shugaban hukumar kula da asusun, ya bayyana cewa ‘ayyukan masu safarar baƙin haure sun ɗauki wani sabon salo da ba za a taɓa amincewa da su ba, don haka ya kamata a yi duk mai yiwuwa wajen ganin an magance.

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

“Taron da muke yi a yau yana ɗaya daga cikin irin ƙoƙarin da muke yi na ganin mun yi wani ƙwaƙƙwaran bayani game da shirye-shiryen da muke yi na ganin masu fasa ƙwaurin baƙin haure sun kwashi kashinsu a hannu.” In ji shi.

Ya sake nanata cewa aikin hukumar asusun yana da tsauri kuma da girma don haka yana buƙatar dogon lokaci, jajircewa da gogewa daga membobin don samun nasara mai kyau a yaƙi da safarar baƙin haure.

NIS
Jami’an NIS a wurin taron

Sashe na 97 na Dokar Shige da Fice ta 2015 ya tanadi kafa Asusun Tallafa Wa Baƙin Haure wanda zai riƙa samun kuɗaɗen gudanarwa daga duk abin da aka samu na dukiya da sayar da kadarorin masu safarar baƙin hauren bisa sahalewar kotu.

Har ila yau, ya tanadi cewa Hukumar Gudanarwa na Asusun za ta ƙunshi wakilai daga: Ma’aikatar Cikin Gida; Kwanturola Janar na Hukumar Shige da Fice (NIS) a matsayin shugaba; Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya; Ma’aikatar Kudi ta Tarayya; Ma’aikatar Harkokin Mata da Ci gaban Al’umma ta Tarayya da Ofishin Akanta-Janar.
Sauran sun haɗa da: Ofishin Babban Mai Binciken Kuɗi; Babban Bankin Nijeriya; da kuma Hukumar Hana Fataucin Bil’adama ta ƙasa (NAPTIP) da sauransu.

Cikin manyan abubuwan da aka gudanar a taron akwai ƙaddamar da wakilan asusun daga ma’aikatu da hukumomin da suka haɗa da: Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, da ta Harkokin Mata da Ci gaban Jama’a, da NAPTIP, da Ofishin Akanta-Janar da sauran wadanda Mista Peter Obodo mai wakiltar ma’aikatar cikin gida ya gabatar.

Ƙaddamar da Hukumar Gudanarwar Asusun dai, na nuna an sake ayyana yaƙi da masu safarar baƙin haure da haramtattun kadarorinsu cikin sabon salo da zai zama mai alfanu a bisa jagorancin shugaban hukumar ta NIS, CGI Isah Jere Idris.

 

NIS
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Farashin Alkama Ya Sauka a Duniya

Farashin Alkama Ya Sauka a Duniya

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.