• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Ƙaddamar Da Hukumar Gudanarwar Asusun Kula Da Baƙin Haure

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Labarai
0
NIS Ta Ƙaddamar Da Hukumar Gudanarwar Asusun Kula Da Baƙin Haure
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa yaƙi da safarar baƙin haure, Hukumar Kula da Shige da Fice ta ƙasa (NIS) ta ƙaddamar da hukumar kula da asusun kula da ayyukan fasa ƙwaurin baƙin haure a hedikwatarta da ke Abuja.

  • Tikitin Tinubu Da Shettima: Yadda Tarihi Ya Maimaita Kansa

ƙaddamarwar tana nuna wani gagarumin ci gaba a ƙudurin da NIS take da shi na ba wai kawai yaƙi da mutanen da ke yin safarar baƙin haure ba har ma da tabbatar da cewa waɗanda aka ceto daga masu safarar baƙin hauren an kula da su don ci gaba da rayuwarsu.

NIS
Shugaban NIS, CGI Isah Jere Idris tare da wakilin Ministan Cikin Gida, Mista Peter Obodo

Da yake jawabi jim kaɗan bayan ƙaddamar da hukumar, Ministan harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola wanda wani Darakta a ma’aikatar Cikin Gida, Mista Peter Obodo ya wakilta, ya yaba wa hukumar bisa kafa wannan asusun tare da yin kira ga mambobin kula da asusun su tashi tsaye wajen yaƙi da ayyukan masu fasa ƙwaurin baƙin haure.

NIS
Yayin ƙaddamar da Hukumar Kula da Asusun

Ya nunar da cewa daga yanzu, masu safarar baƙin haure ba za su ci gaba da cin karensu ba babbaka ba kamar yadda suka saba.

Tun da farko a nasa jawabin, Shugaban NIS, CGI Isah Jere Idris wanda shi ne shugaban hukumar kula da asusun, ya bayyana cewa ‘ayyukan masu safarar baƙin haure sun ɗauki wani sabon salo da ba za a taɓa amincewa da su ba, don haka ya kamata a yi duk mai yiwuwa wajen ganin an magance.

Labarai Masu Nasaba

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

“Taron da muke yi a yau yana ɗaya daga cikin irin ƙoƙarin da muke yi na ganin mun yi wani ƙwaƙƙwaran bayani game da shirye-shiryen da muke yi na ganin masu fasa ƙwaurin baƙin haure sun kwashi kashinsu a hannu.” In ji shi.

Ya sake nanata cewa aikin hukumar asusun yana da tsauri kuma da girma don haka yana buƙatar dogon lokaci, jajircewa da gogewa daga membobin don samun nasara mai kyau a yaƙi da safarar baƙin haure.

NIS
Jami’an NIS a wurin taron

Sashe na 97 na Dokar Shige da Fice ta 2015 ya tanadi kafa Asusun Tallafa Wa Baƙin Haure wanda zai riƙa samun kuɗaɗen gudanarwa daga duk abin da aka samu na dukiya da sayar da kadarorin masu safarar baƙin hauren bisa sahalewar kotu.

Har ila yau, ya tanadi cewa Hukumar Gudanarwa na Asusun za ta ƙunshi wakilai daga: Ma’aikatar Cikin Gida; Kwanturola Janar na Hukumar Shige da Fice (NIS) a matsayin shugaba; Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya; Ma’aikatar Kudi ta Tarayya; Ma’aikatar Harkokin Mata da Ci gaban Al’umma ta Tarayya da Ofishin Akanta-Janar.
Sauran sun haɗa da: Ofishin Babban Mai Binciken Kuɗi; Babban Bankin Nijeriya; da kuma Hukumar Hana Fataucin Bil’adama ta ƙasa (NAPTIP) da sauransu.

Cikin manyan abubuwan da aka gudanar a taron akwai ƙaddamar da wakilan asusun daga ma’aikatu da hukumomin da suka haɗa da: Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, da ta Harkokin Mata da Ci gaban Jama’a, da NAPTIP, da Ofishin Akanta-Janar da sauran wadanda Mista Peter Obodo mai wakiltar ma’aikatar cikin gida ya gabatar.

Ƙaddamar da Hukumar Gudanarwar Asusun dai, na nuna an sake ayyana yaƙi da masu safarar baƙin haure da haramtattun kadarorinsu cikin sabon salo da zai zama mai alfanu a bisa jagorancin shugaban hukumar ta NIS, CGI Isah Jere Idris.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tikitin Tinubu Da Shettima: Yadda Tarihi Ya Maimaita Kansa

Next Post

Farashin Alkama Ya Sauka a Duniya

Related

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Labarai

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

5 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

5 hours ago
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
Labarai

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

6 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

8 hours ago
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

8 hours ago
Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba
Labarai

Ba Gaskiya Ba Ne: Ɓarayi Ba Su Sace Ɗan Uwan Gwamnan Zamfara Ba

10 hours ago
Next Post
Farashin Alkama Ya Sauka a Duniya

Farashin Alkama Ya Sauka a Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.