• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Karrama Jami’an Da Suka Nuna Bajinta A2022

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
in Labarai
0
NIS

Wani mazaunin manyan baƙi

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice ta ƙasa (NIS), ta karrama wasu zaƙaƙuran jami’anta sama da 40 da suka nuna bajinta a fagen aiki, a wata liyafar abincin dare ta ƙarshen shekarar 2022, da ta saba shiryawa a duk shekara.

An karrama jami’an ne a yayin liyafar da ta gudana a shalkwatar hukumar ranar Juma’ar nan.

Da yake jawabi a bikin, Kwanturola Janar na NIS, Isah Jere Idris ya bayyana cewa an karrama jami’an ne bisa cancanta inda ya yi kira gare su, su ruɓanya ƙwazonsu domin saka wannan karamci da aka yi musu kana ya hori waɗanda ba su samu ba su ƙara himma domin ganin sun shiga cikin waɗanda suka cancanta a baɗi idan Allah ya kai mu.

Karrama
Har ila yau, ya ce, baya ga waɗanda aka karrama akwai kuma waɗanda aka hukunta daban-daban bisa samun su da hannu a laifukan da suka shafi zamba ta ɗaukar aiki da sauransu. “An kori jami’ai 8, an hukunta 18, sannan akwai wasu da ake kan bincike a kansu.” In ji shi.

  • Na Yi Bakin Kokarina A Matsayin Shugaban Nijeriya — Buhari

 

Labarai Masu Nasaba

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

Da yake tsokaci kan nasarorin da hukumar ta samu a 2022, CGI Isah Jere ya ce an samu ƙarin cibiyoyin fasfo da aka mayar da su tsarin sabon fasfo da aka inganta a zamanance, a ciki da wajen ƙasar nan, kana ya ba da tabbacin ci gaba da yin haka har a kai ga mayar da ɗaukacin cibiyoyin fasfo a ƙarƙashin sabon tsarin.

NIS
CGI Isah Jere Idris yayin da yake jawabi

Dangane da batun kyautata walwalar jami’ai kuwa, Isah Jere ya bayyana cewa akwai manyan jami’ai guda 5 da aka ƙara musu girma zuwa matsayin manyan mataimakan Kwanturola Janar, sannan ya ce zai yi tsayin daka wajen ganin an fitar da sakamakon jarrabawar ƙarin girma da aka yi wa sauran jami’ai domin a samu ƙarin waɗanda za a ciyar da su gaba.
Wakazalika, CGI Isah Jere ya bayyana cewa a ɓangaren tsaron iyaloki, sun ɗauki ƙarin matakai daban-daban, yana mai cewar, “Mun ziyarci NIMASA mun tattauna a kan ƙarfafa tsaron iyaka, yanzu haka da nake magana da ku an kammala yarjejeniyar da za mu rattaba hannu da su. Haka nan ba da jimawa ba, muka yaye wasu dakaru mata 61 da za mu tura su aikin tsaron iyalokin ƙasa baya ga sauran matakai na aiki da na’urorin zamani da muke ci gaba da ɗaukawa don tabbatar da tsaron iyaka.”
Isah Jere ya sa an yi tsit na minti ɗaya domin girmamawa ga jaruman dakarun NIS da suka rasa rayukansu a bakin aiki wajen tabbatar da tsaron iyaka.

Karrama
Mahalarta

Har ila yau, ya yi bayanin cewa
Ya ƙaddamar da shirin samar da gidaje kuma ba da jimawa ba za a fara rabawa ta hanyar ƙungiyar gama kai ta jami’an NIS domin ƙara kyautata jin daɗin jami’ai.

Ya gode wa Shugaba Buhari bisa goyon bayan da yake bai wa NIS na tsawon lokaci. Haka nan ya gode wa Ministan Cikin Gida, Rauf Aregbesola da babban sakataren ma’aikatar tare da dukkan mambobin hukumar gudanarwar ma’aikatar bisa tallafa wa samun nasarorin hukumar.

NIS
Mahalarta

A nashi ɓangaren, wakilin ministan cikin gida, Janar Bassey mai ritaya, ya bayyana cewa, tun lokacin da aka naɗa shi a matsayin kwamuishina a hukumar gudanarwar ma’aikatar cikin gida, NIS ce kawai take shirya irin wannan biki, kana ya yi kira ga sauran takwarorinta su yi koyi.

Ya yaba wa CGI Isah Jere Idris bisa ƙoƙarin kawo sauyi da yake yi tun lokacin da ya karɓi ragama, inda ya buƙace shi ya ci gaba da hakan.
Ya ce minista yana taya ɗaukacin ‘Yan Nijeriya murnar bikin Kirsimeti da na sabuwar shekara ta 2023.

Shi kuwa DCG Haliru wanda ya yi jawabin godiya, ya yi kira ga waɗanda suka samu lambobin yabon kar su ɗauki lamarin a matsayin abin da za su shantake, amma su ƙara himma da ƙwazo.
Haka nan ya yi kiran haɗin gwiwa a tsakanin rundunonin tsaro domin samun ƙarin nasara a kan sha’anin tsaron ƙasa.

Haliru ya ƙara da cewa, a zamanin shugabancin CGI Jere sun samu lambobin yabo guda 5, wanda ba a taɓa bai wa wani mai muƙamin DCG Lambar Yabo ta ƙasa (MFR) ba sai a zamaninsa.
Ya nemi jami’ai su yafe wa juna idan akwai laifi a tsakaninsu, kana su ƙara haɗin kai domin aiki ya tafi daidai wa daida.
ɗaya daga cikin waɗanda aka bai wa lambar yabon, ya yi godiya ga NIS a madadin saura, “da ta ga cewa mun dace ta karrama mu, kuma muna ƙara jaddada cewa za mu ƙara zage damtse mu ci gaba da aiki tuƙuru.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Bude Bangare Na 2 Na Taron Kare Mabanbantan Halittu Na COP15

Next Post

Jerin ‘Yan Kwallon Da Suka Buga Wasanni Da Yawa A Gasar Kofin Duniya

Related

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

29 minutes ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

3 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

4 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

4 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

5 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

7 hours ago
Next Post
Jerin ‘Yan Kwallon Da Suka Buga Wasanni Da Yawa A Gasar Kofin Duniya

Jerin 'Yan Kwallon Da Suka Buga Wasanni Da Yawa A Gasar Kofin Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.