• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Karrama Jami’an Da Suka Nuna Bajinta A2022

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Labarai
0
NIS

Wani mazaunin manyan baƙi

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice ta ƙasa (NIS), ta karrama wasu zaƙaƙuran jami’anta sama da 40 da suka nuna bajinta a fagen aiki, a wata liyafar abincin dare ta ƙarshen shekarar 2022, da ta saba shiryawa a duk shekara.

An karrama jami’an ne a yayin liyafar da ta gudana a shalkwatar hukumar ranar Juma’ar nan.

Da yake jawabi a bikin, Kwanturola Janar na NIS, Isah Jere Idris ya bayyana cewa an karrama jami’an ne bisa cancanta inda ya yi kira gare su, su ruɓanya ƙwazonsu domin saka wannan karamci da aka yi musu kana ya hori waɗanda ba su samu ba su ƙara himma domin ganin sun shiga cikin waɗanda suka cancanta a baɗi idan Allah ya kai mu.

Karrama
Har ila yau, ya ce, baya ga waɗanda aka karrama akwai kuma waɗanda aka hukunta daban-daban bisa samun su da hannu a laifukan da suka shafi zamba ta ɗaukar aiki da sauransu. “An kori jami’ai 8, an hukunta 18, sannan akwai wasu da ake kan bincike a kansu.” In ji shi.

  • Na Yi Bakin Kokarina A Matsayin Shugaban Nijeriya — Buhari

 

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

Da yake tsokaci kan nasarorin da hukumar ta samu a 2022, CGI Isah Jere ya ce an samu ƙarin cibiyoyin fasfo da aka mayar da su tsarin sabon fasfo da aka inganta a zamanance, a ciki da wajen ƙasar nan, kana ya ba da tabbacin ci gaba da yin haka har a kai ga mayar da ɗaukacin cibiyoyin fasfo a ƙarƙashin sabon tsarin.

NIS
CGI Isah Jere Idris yayin da yake jawabi

Dangane da batun kyautata walwalar jami’ai kuwa, Isah Jere ya bayyana cewa akwai manyan jami’ai guda 5 da aka ƙara musu girma zuwa matsayin manyan mataimakan Kwanturola Janar, sannan ya ce zai yi tsayin daka wajen ganin an fitar da sakamakon jarrabawar ƙarin girma da aka yi wa sauran jami’ai domin a samu ƙarin waɗanda za a ciyar da su gaba.
Wakazalika, CGI Isah Jere ya bayyana cewa a ɓangaren tsaron iyaloki, sun ɗauki ƙarin matakai daban-daban, yana mai cewar, “Mun ziyarci NIMASA mun tattauna a kan ƙarfafa tsaron iyaka, yanzu haka da nake magana da ku an kammala yarjejeniyar da za mu rattaba hannu da su. Haka nan ba da jimawa ba, muka yaye wasu dakaru mata 61 da za mu tura su aikin tsaron iyalokin ƙasa baya ga sauran matakai na aiki da na’urorin zamani da muke ci gaba da ɗaukawa don tabbatar da tsaron iyaka.”
Isah Jere ya sa an yi tsit na minti ɗaya domin girmamawa ga jaruman dakarun NIS da suka rasa rayukansu a bakin aiki wajen tabbatar da tsaron iyaka.

Karrama
Mahalarta

Har ila yau, ya yi bayanin cewa
Ya ƙaddamar da shirin samar da gidaje kuma ba da jimawa ba za a fara rabawa ta hanyar ƙungiyar gama kai ta jami’an NIS domin ƙara kyautata jin daɗin jami’ai.

Ya gode wa Shugaba Buhari bisa goyon bayan da yake bai wa NIS na tsawon lokaci. Haka nan ya gode wa Ministan Cikin Gida, Rauf Aregbesola da babban sakataren ma’aikatar tare da dukkan mambobin hukumar gudanarwar ma’aikatar bisa tallafa wa samun nasarorin hukumar.

NIS
Mahalarta

A nashi ɓangaren, wakilin ministan cikin gida, Janar Bassey mai ritaya, ya bayyana cewa, tun lokacin da aka naɗa shi a matsayin kwamuishina a hukumar gudanarwar ma’aikatar cikin gida, NIS ce kawai take shirya irin wannan biki, kana ya yi kira ga sauran takwarorinta su yi koyi.

Ya yaba wa CGI Isah Jere Idris bisa ƙoƙarin kawo sauyi da yake yi tun lokacin da ya karɓi ragama, inda ya buƙace shi ya ci gaba da hakan.
Ya ce minista yana taya ɗaukacin ‘Yan Nijeriya murnar bikin Kirsimeti da na sabuwar shekara ta 2023.

Shi kuwa DCG Haliru wanda ya yi jawabin godiya, ya yi kira ga waɗanda suka samu lambobin yabon kar su ɗauki lamarin a matsayin abin da za su shantake, amma su ƙara himma da ƙwazo.
Haka nan ya yi kiran haɗin gwiwa a tsakanin rundunonin tsaro domin samun ƙarin nasara a kan sha’anin tsaron ƙasa.

Haliru ya ƙara da cewa, a zamanin shugabancin CGI Jere sun samu lambobin yabo guda 5, wanda ba a taɓa bai wa wani mai muƙamin DCG Lambar Yabo ta ƙasa (MFR) ba sai a zamaninsa.
Ya nemi jami’ai su yafe wa juna idan akwai laifi a tsakaninsu, kana su ƙara haɗin kai domin aiki ya tafi daidai wa daida.
ɗaya daga cikin waɗanda aka bai wa lambar yabon, ya yi godiya ga NIS a madadin saura, “da ta ga cewa mun dace ta karrama mu, kuma muna ƙara jaddada cewa za mu ƙara zage damtse mu ci gaba da aiki tuƙuru.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Bude Bangare Na 2 Na Taron Kare Mabanbantan Halittu Na COP15

Next Post

Jerin ‘Yan Kwallon Da Suka Buga Wasanni Da Yawa A Gasar Kofin Duniya

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

8 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

11 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

13 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

14 hours ago
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki
Labarai

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

16 hours ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

17 hours ago
Next Post
Jerin ‘Yan Kwallon Da Suka Buga Wasanni Da Yawa A Gasar Kofin Duniya

Jerin 'Yan Kwallon Da Suka Buga Wasanni Da Yawa A Gasar Kofin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Karrama

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.