• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Yi Kawance Da NAPTIP Da IOM Domin Horas Da Jami’anta

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
in Labarai
0
NIS Ta Yi Kawance Da NAPTIP Da IOM Domin Horas Da Jami’anta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula Da Shige Da Fice ta Kasa (NIS) ta yi kawance da takwararta ta duniya (IOM), da Hukumar Yaki Da Safarar Bil’adama (NAPTIP) da Sashen Ayyyukan Lafiya na PHS, wajen shirya wani taron kara wa juna sani da nufin samar da horo da dabarun aiki ga jami’anta.

An shirya horaswar ce a karkashin shirin da aka yi wa sunan TSI a takaice.

  • Yadda Ango Ya Yi Shahada Wajen Kare Amaryarsa Daga ‘Yan Bindiga

A wata sanarwa da Jami’in hulda da jama’a na NIS, Amos Okpu ya fitar, NIS ta bayyana cewa shirin yana samun tallafin hukumar kula da shige da fice ta duniya (IOM) da nufin bunkasa ayyuka a iyakokin kasa da kara sanya ido kan harkokin shige da fice a Nijeriya tare da taimaka wa hukumomin kula da shige da fice.

Shirin na da manufar bunkasa kwazo da hazakar jami’an da ke aiki a hukumomin dakile safarar mutane da shige da fice ta barauniyar hanya domin ayyuka su rika tafiya yadda ya dace a kowane lokaci.

NIS

Labarai Masu Nasaba

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

Da yake jawabi a wajen kaddamar da shirin karo na na biyu, Shugaban Hukumar ta NIS, Isah Jere Idris, wanda ya samu wakilcin mataimakin kwanturola Janar mai kula da harkokin biza, Ishaka Abdulmumini Haliru, ya misalta kokarin abokan hukumar wajen kara bunkasa kwazon aikin jami’an NIS da NAPTIP a matsayin wani gagarumin ci gaba da zai kyautata harkokin shige da fice da dakile yawan safarar mutane ta barauniyar hanya, yana mai cewa hakan zai kara kyautata alaka a tsakanin bangarorin.

Ya ce, a kowani lokaci suna kula sosai da ba da fifiko ga sashin horar da jami’ansu domin tabbatar da ayyuka na gudana yadda ya dace, kan haka ne ma ya nuna farin cikinsa da wannan shirin.

NIS

A nata jawabin, darakta-janar ta Hukumar NAPTIP, Dakta Fatima Waziri-Azir, ta ce, IOM na tallafa wa shirye-shiryen da ke inganta kwazon jami’ai a fagen aiki a-kai-a-kai.

Ta yi kira ga hukumomi da jami’an da abin ya shafa da su yi amfani da wannan damar tallafin da suke samu daga kungiyoyin kasashen waje wajen inganta ayyukansu a kowani lokaci.

Sannan, ta bukaci jami’an NIS da NAPTIP da su ci gaba da kyautata alakar aiki mai inganci a tsakaninsu domin hada karfi da karfe waje guda don yaki da safarar mutane da jigila ta kai-komo ta barauniyar hanya.

Shi kuma a bangarensa, daraktan ayyukan lafiya na PHS, Dakta Geoffrey Okatubo, ya ce a ‘yan kwanakin baya sashen kula da lafiya ya fuskanci barazanar annobar korona da aka fuskanta, a yanzu kuma ga cutar kyandar biri (Monkey pox) da ake fama da ita a halin yanzu.

Sai ya nuna kwarin guiwarsa na cewa da hadin guiwar abokan aiki na cikin kasar Nijeriya da kasashen waje ana samun sakamako mai kyau wajen kula da lafiya.

NIS

Shugaban NIS, Isah Idris Jere ya sha nanata cewa zai mayar da hankali ga horas da jami’a domin inganta ayyukan hukumar a kowane sashe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Dan Nijeriya Ya Harbe Matarsa Da Kakarsa, Ya Kuma Kashe Kansa A Amurka

Next Post

Kwamitin tantance ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da ‘Yan Takara 10 Cikin 23

Related

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi

6 minutes ago
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

9 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

10 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

11 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

12 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

14 hours ago
Next Post
Kwamitin tantance ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da ‘Yan Takara 10 Cikin 23

Kwamitin tantance 'Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da 'Yan Takara 10 Cikin 23

LABARAI MASU NASABA

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.