ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Yi Kawance Da NAPTIP Da IOM Domin Horas Da Jami’anta

by Abdulrazaq Yahuza
4 years ago
NIS

Hukumar Kula Da Shige Da Fice ta Kasa (NIS) ta yi kawance da takwararta ta duniya (IOM), da Hukumar Yaki Da Safarar Bil’adama (NAPTIP) da Sashen Ayyyukan Lafiya na PHS, wajen shirya wani taron kara wa juna sani da nufin samar da horo da dabarun aiki ga jami’anta.

An shirya horaswar ce a karkashin shirin da aka yi wa sunan TSI a takaice.

  • Yadda Ango Ya Yi Shahada Wajen Kare Amaryarsa Daga ‘Yan Bindiga

A wata sanarwa da Jami’in hulda da jama’a na NIS, Amos Okpu ya fitar, NIS ta bayyana cewa shirin yana samun tallafin hukumar kula da shige da fice ta duniya (IOM) da nufin bunkasa ayyuka a iyakokin kasa da kara sanya ido kan harkokin shige da fice a Nijeriya tare da taimaka wa hukumomin kula da shige da fice.

ADVERTISEMENT

Shirin na da manufar bunkasa kwazo da hazakar jami’an da ke aiki a hukumomin dakile safarar mutane da shige da fice ta barauniyar hanya domin ayyuka su rika tafiya yadda ya dace a kowane lokaci.

NIS

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Da yake jawabi a wajen kaddamar da shirin karo na na biyu, Shugaban Hukumar ta NIS, Isah Jere Idris, wanda ya samu wakilcin mataimakin kwanturola Janar mai kula da harkokin biza, Ishaka Abdulmumini Haliru, ya misalta kokarin abokan hukumar wajen kara bunkasa kwazon aikin jami’an NIS da NAPTIP a matsayin wani gagarumin ci gaba da zai kyautata harkokin shige da fice da dakile yawan safarar mutane ta barauniyar hanya, yana mai cewa hakan zai kara kyautata alaka a tsakanin bangarorin.

Ya ce, a kowani lokaci suna kula sosai da ba da fifiko ga sashin horar da jami’ansu domin tabbatar da ayyuka na gudana yadda ya dace, kan haka ne ma ya nuna farin cikinsa da wannan shirin.

NIS

A nata jawabin, darakta-janar ta Hukumar NAPTIP, Dakta Fatima Waziri-Azir, ta ce, IOM na tallafa wa shirye-shiryen da ke inganta kwazon jami’ai a fagen aiki a-kai-a-kai.

Ta yi kira ga hukumomi da jami’an da abin ya shafa da su yi amfani da wannan damar tallafin da suke samu daga kungiyoyin kasashen waje wajen inganta ayyukansu a kowani lokaci.

Sannan, ta bukaci jami’an NIS da NAPTIP da su ci gaba da kyautata alakar aiki mai inganci a tsakaninsu domin hada karfi da karfe waje guda don yaki da safarar mutane da jigila ta kai-komo ta barauniyar hanya.

Shi kuma a bangarensa, daraktan ayyukan lafiya na PHS, Dakta Geoffrey Okatubo, ya ce a ‘yan kwanakin baya sashen kula da lafiya ya fuskanci barazanar annobar korona da aka fuskanta, a yanzu kuma ga cutar kyandar biri (Monkey pox) da ake fama da ita a halin yanzu.

Sai ya nuna kwarin guiwarsa na cewa da hadin guiwar abokan aiki na cikin kasar Nijeriya da kasashen waje ana samun sakamako mai kyau wajen kula da lafiya.

NIS

Shugaban NIS, Isah Idris Jere ya sha nanata cewa zai mayar da hankali ga horas da jami’a domin inganta ayyukan hukumar a kowane sashe.

NIS
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
Kwamitin tantance ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da ‘Yan Takara 10 Cikin 23

Kwamitin tantance 'Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da 'Yan Takara 10 Cikin 23

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.