• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Yi Wa Manyan Jami’ai 98 Ado Da Sabbin Muƙamansu

by yahuzajere
3 years ago
in Labarai
0
NIS Ta Yi Wa Manyan Jami’ai 98 Ado Da Sabbin Muƙamansu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), CGI Isah Idris Jere ya yi wa manyan jami’ai 94 da suka samu ƙarin girma ado da sababbin muƙamansu a shalkwatar hukumar da ke Abuja, yayin da ragowar huxun aka yi musu a Ma’aikatar Cikin Gida.

Wannan ya biyo bayan amincewa da ƙarin girma ga manyan jami’an ne da Hukumar Gudanarwar Rundunonin Ma’aikatar Cikin Gida (CDCFIB) ta yi tare da fitar da sunayen waxanda suka samu a shekarar 2022 a can kwanan baya.

  • Atiku Zai Yi Wa Tinubu Kwab Ɗaya, Don Ba Tsaransa Ba Ne, In Ji PDP

Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulxa da jama’a na NIS, ACI Amos Okpu ta bayyana cewa jimillar sabbin waxanda aka ƙara wa girma zuwa muƙamin ƙananan mataimakan Kwanturola Janar 24 da Kwanturololi 70 aka yi musu ado da sabbin muƙaman a wani ƙwarya-ƙwaryan biki da ya samu halartar takwarorin NIS da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Cikin Gida da sauran manyan jagororin Hukumar CDCFIB.

NIS

Da yake jawabi a wurin, Shugaban NIS, Isah Jere ya bayyana cewa ƙarin girman da jami’an suka samu ya nuna ɓaro-ɓaro a fili irin yadda hukumar ta mayar da hankali ga inganta walwalar jami’anta. Ya nunar da cewa wannan yana daga cikin manyan ƙudurori uku da yake son cimmawa tun daga lokacin da ya karɓi ragamar shugabancin hukumar da suka haxa da inganta tsaron iyakokin ƙasa, gyarar fuska ga ayyukan fasfo sai kuma kyautata jin daxi da walwalar jami’ai.

Labarai Masu Nasaba

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

NIS

Ya hori sabbin jami’an da suka samu ƙarin girman su ƙara duƙufa sosai ga aiki da kula da ayyukan na ƙasa da su domin tabbatar da ayyuka sun inganta a hukumar a samu xorewar ci gaban da ake samu. Ya ƙara da cewa, hukumar ba za ta lamunci raggonci ba daga gare su musamman ta ɓangaren da ake ganin ana iya cimma nasara xari bisa xari.

Tun da farko dai, Sakatariyar Hukumar Gudanarwa ta CDCFIB, Hajiya Aisha Rufa’i ta taya sabbin masu muƙaman murna bisa ci gaban da suka samu ta la’akari da cancanta, tana mai jaddada cewa hukumar ta yi nazari sosai a kan halaye da xabi’unsu, da ƙwazonsu na aiki da iya zance da sauran dabarun da ake buƙatar gani kafin a yi wa manyan jami’ai ƙarin girma.

NIS

Wakazalika, shi ma Kwamishinan Hukumar Gudanarwar mai kula da xaukar aiki da ƙarin girma, Manjo Janar Emmanuel Bassey mai ritaya, ya yi kira ga jami’an da aka ƙara wa girman su jagoranci sauran ma’aikata da ke ƙarƙashinsu cikin dattaku da kamun kai sannan a koyaushe ya zama suna cikin shirin aiki bisa ƙwarewa da xa’a a matsayinsu na manyan jami’ai.

Daga cikin manyan jami’an da aka saka musu sabbin muƙaman nasu na ƙananan mataimakan Kwanturola Janar akwai ACG Kemi Nandap, babbar jami’ar da ke kula da shige da fice a Filin Jiragen Sama na Murtala Muhammad da ke Legas, da babban jami’in harkokin ofishin CGI da aka sauya kwanan nan, ACG Ahmad Bauchi Aliyu da kuma Kwanturola Mustapha Ahmad, mataimaki na musamman ga CGI a fannin gudanar da ayyuka.

A halin da ake ciki kuma, Ministan Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola a ranar Talata ya sanya wa sababbin jami’ai da aka naxa a matsayin manyan mataimakan Kwanturola Janar muƙamansu, a babban xakin taro na ma’aikatar. Waxanda aka yi wa ado da muƙaman sun haxa da DCG Oluremi Talabi, DCG Josephine Kwazu, DCG Modupe Anyalechi da kuma DCG Muhammad Aminu Muhammad.

NIS

Ministan ya taya su murna a kan sabbin muƙaman nasu kana ya nemi su yi amfani da basirarsu da ƙwarewar aiki wajen yaƙi da rashin tsaro a ƙasar nan.

Daga cikin manyan mutanen da suka halarci bikin maƙala sabbin muƙaman na NIS akwai Kwamishinan Tarayya na Hukumar Gudanarwa ta CDCFIB, ACG Ado Jaffaru (mai ritaya), da Sanata Uba Sani, da Sakataren Gwamnatin Jihar Kaduna, Malam Bala Abbas Lawal, da wakilan shugabannin rundunonin da ke ƙarƙashin ma’aikatar cikin gida da sauransu.

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Atiku Zai Yi Wa Tinubu Kwab Ɗaya, Don Ba Tsaransa Ba Ne, In Ji PDP

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Samu Naira Biliyan 19.2 Daga Fannin Zinare A Kwatar Shekara

Related

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC
Labarai

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

26 minutes ago
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar
Manyan Labarai

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

4 hours ago
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne
Labarai

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

6 hours ago
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)
Labarai

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

7 hours ago
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
Labarai

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

8 hours ago
Labarai

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

20 hours ago
Next Post
NIS

Gwamnatin Tarayya Ta Samu Naira Biliyan 19.2 Daga Fannin Zinare A Kwatar Shekara

LABARAI MASU NASABA

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

May 11, 2025
Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

May 11, 2025
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

May 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

May 11, 2025
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

May 11, 2025
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

May 11, 2025
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.