ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Na Zargin Kwankwaso Da Hannu Wajen Nasarar Gawuna Da Kwace Zaben Kano A Kotu

by Muhammad
2 years ago
Kwankwaso

Jam’iyyar NNPP ta zargi tsohon dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Rabiu Kwankwaso, da hannu kan rashin nasarar da gwamnan Kano, Yusuf Abba, ya samu a kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar.

Jam’iyyar ta ce Kwankwaso ya sayar da NNPP ga jam’iyya mai mulki ta APC kan tattaunawarsa a batun kujerar minista da ya yi zawarci a gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

  • Jam’iyyar NNPP Ta Dakatar Da Kwankwaso Na Wata 6 Kan Mata Zagon Kasa
  • DA DUMI DUMINSA: Kotu Ta Dakatar Da Korar Kwankwaso Daga Jam’iyyar NNPP

A ranar Laraba ne kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Kano ta kori Abba tare da bayyana dan takarar jam’iyyar APC, Nasiru Gawuna, a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

ADVERTISEMENT

Kotun mai alkalai uku karkashin jagorancin mai shari’a, Oluyemi Akintan-Osadebay, ta janye takardar shaidar cin zabe da hukumar zabe mai zaman kanta ta bai wa Abba Yusuf.

Da ake bayyana dalilan da suka sa aka tsige gwamnan Kano, kotun ta ce ratar kuri’un da jam’iyyar NNPP ta samu ta samu ne ta haramtacciyar hanya ba ta hanyar da ta dace ba, kuma hanyar da ta bi wajen samun kuri’un basu dace da dokar zabe ta 2022 ba.

LABARAI MASU NASABA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

Alkalan sun cire kuri’u 165,663 daga jam’iyyar NNPP, inda suka kara da cewa a jikin kuri’un guda 165,663 babu sa hannun jami’in zabe da satamfi da kwanan wata kamar yadda doka ta tanada, don haka suka bayyana cewa kuri’un ba su da inganci.

Da yake mayar da martani, daya daga cikin jagororin jam’iyyar NNPP a yankin Kudu maso Yamma, Alhaji Abass Akande Onilewura, a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Alhamis, ya ce rashi da jam’iyyar ta yi a Kano ya tabbatar da zargin kin jinin jam’iyyar da aka yi saboda Kwankwaso.

Onilewura ya jaddada cewa tsohon dan takarar jam’iyyar NNPP na da hannu dumu-dumu da hadin baki da Jam’iyyar APC wanda hakan ya haifar da babban rashi da jam’iyyar ke fuskanta kotunan zabe a Kano.

Ya nanata cewa Kwankwaso bai bi ka’ida ba wajen zabar wasu daga cikin ‘yan takara a jam’iyyar, lamarin da ya ce ya kai shigar da Jam’iyyar cikin halin da ta samu kanta a yanzu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama
Manyan Labarai

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama

November 15, 2025
Next Post
Annabi

Sabon Karatu: Tsantseni Da Gudun Duniya Na Annabi (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.