• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Na Zargin Kwankwaso Da Hannu Wajen Nasarar Gawuna Da Kwace Zaben Kano A Kotu

by Muhammad
2 years ago
Kwankwaso

Jam’iyyar NNPP ta zargi tsohon dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Rabiu Kwankwaso, da hannu kan rashin nasarar da gwamnan Kano, Yusuf Abba, ya samu a kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar.

Jam’iyyar ta ce Kwankwaso ya sayar da NNPP ga jam’iyya mai mulki ta APC kan tattaunawarsa a batun kujerar minista da ya yi zawarci a gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

  • Jam’iyyar NNPP Ta Dakatar Da Kwankwaso Na Wata 6 Kan Mata Zagon Kasa
  • DA DUMI DUMINSA: Kotu Ta Dakatar Da Korar Kwankwaso Daga Jam’iyyar NNPP

A ranar Laraba ne kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Kano ta kori Abba tare da bayyana dan takarar jam’iyyar APC, Nasiru Gawuna, a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

Kotun mai alkalai uku karkashin jagorancin mai shari’a, Oluyemi Akintan-Osadebay, ta janye takardar shaidar cin zabe da hukumar zabe mai zaman kanta ta bai wa Abba Yusuf.

Da ake bayyana dalilan da suka sa aka tsige gwamnan Kano, kotun ta ce ratar kuri’un da jam’iyyar NNPP ta samu ta samu ne ta haramtacciyar hanya ba ta hanyar da ta dace ba, kuma hanyar da ta bi wajen samun kuri’un basu dace da dokar zabe ta 2022 ba.

LABARAI MASU NASABA

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Alkalan sun cire kuri’u 165,663 daga jam’iyyar NNPP, inda suka kara da cewa a jikin kuri’un guda 165,663 babu sa hannun jami’in zabe da satamfi da kwanan wata kamar yadda doka ta tanada, don haka suka bayyana cewa kuri’un ba su da inganci.

Da yake mayar da martani, daya daga cikin jagororin jam’iyyar NNPP a yankin Kudu maso Yamma, Alhaji Abass Akande Onilewura, a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Alhamis, ya ce rashi da jam’iyyar ta yi a Kano ya tabbatar da zargin kin jinin jam’iyyar da aka yi saboda Kwankwaso.

Onilewura ya jaddada cewa tsohon dan takarar jam’iyyar NNPP na da hannu dumu-dumu da hadin baki da Jam’iyyar APC wanda hakan ya haifar da babban rashi da jam’iyyar ke fuskanta kotunan zabe a Kano.

Ya nanata cewa Kwankwaso bai bi ka’ida ba wajen zabar wasu daga cikin ‘yan takara a jam’iyyar, lamarin da ya ce ya kai shigar da Jam’iyyar cikin halin da ta samu kanta a yanzu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai
Manyan Labarai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya
Manyan Labarai

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Next Post
Annabi

Sabon Karatu: Tsantseni Da Gudun Duniya Na Annabi (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.