• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Na Zargin Kwankwaso Da Hannu Wajen Nasarar Gawuna Da Kwace Zaben Kano A Kotu

by Muhammad
2 years ago
in Manyan Labarai, Siyasa
0
NNPP Ta Maka Kwankwaso A Kotu Kan Zargin Yi Wa Jam’iyya Makarkashiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar NNPP ta zargi tsohon dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Rabiu Kwankwaso, da hannu kan rashin nasarar da gwamnan Kano, Yusuf Abba, ya samu a kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar.

Jam’iyyar ta ce Kwankwaso ya sayar da NNPP ga jam’iyya mai mulki ta APC kan tattaunawarsa a batun kujerar minista da ya yi zawarci a gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

  • Jam’iyyar NNPP Ta Dakatar Da Kwankwaso Na Wata 6 Kan Mata Zagon Kasa
  • DA DUMI DUMINSA: Kotu Ta Dakatar Da Korar Kwankwaso Daga Jam’iyyar NNPP

A ranar Laraba ne kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Kano ta kori Abba tare da bayyana dan takarar jam’iyyar APC, Nasiru Gawuna, a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

Kotun mai alkalai uku karkashin jagorancin mai shari’a, Oluyemi Akintan-Osadebay, ta janye takardar shaidar cin zabe da hukumar zabe mai zaman kanta ta bai wa Abba Yusuf.

Da ake bayyana dalilan da suka sa aka tsige gwamnan Kano, kotun ta ce ratar kuri’un da jam’iyyar NNPP ta samu ta samu ne ta haramtacciyar hanya ba ta hanyar da ta dace ba, kuma hanyar da ta bi wajen samun kuri’un basu dace da dokar zabe ta 2022 ba.

Labarai Masu Nasaba

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

Alkalan sun cire kuri’u 165,663 daga jam’iyyar NNPP, inda suka kara da cewa a jikin kuri’un guda 165,663 babu sa hannun jami’in zabe da satamfi da kwanan wata kamar yadda doka ta tanada, don haka suka bayyana cewa kuri’un ba su da inganci.

Da yake mayar da martani, daya daga cikin jagororin jam’iyyar NNPP a yankin Kudu maso Yamma, Alhaji Abass Akande Onilewura, a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Alhamis, ya ce rashi da jam’iyyar ta yi a Kano ya tabbatar da zargin kin jinin jam’iyyar da aka yi saboda Kwankwaso.

Onilewura ya jaddada cewa tsohon dan takarar jam’iyyar NNPP na da hannu dumu-dumu da hadin baki da Jam’iyyar APC wanda hakan ya haifar da babban rashi da jam’iyyar ke fuskanta kotunan zabe a Kano.

Ya nanata cewa Kwankwaso bai bi ka’ida ba wajen zabar wasu daga cikin ‘yan takara a jam’iyyar, lamarin da ya ce ya kai shigar da Jam’iyyar cikin halin da ta samu kanta a yanzu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abba Gida-gidakanoKwace Zaben KanoKwankwasoNNPPZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wa Ya Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina?

Next Post

Sabon Karatu: Tsantseni Da Gudun Duniya Na Annabi (SAW)

Related

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

38 minutes ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

2 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

10 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

15 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

21 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

1 day ago
Next Post
Annabi

Sabon Karatu: Tsantseni Da Gudun Duniya Na Annabi (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.