• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noma Tushen Arziki

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Noma Tushen Arziki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matsalar sauyin yanayi abu ne da a ko da yaushe ake ci gaba da tattaunawa kansa a duniya, domin lalubo bakin zaren warware mummunan tasirinta. A ci gaba da hakan ne, masana kimiyya na kasar Sin da na kasashen Afrika suka kira da a samo tsare-tsaren samar da abinci masu jure yanayi don kawar da yunwa a Afrika.

Kaso 2 zuwa 3 na hayaki mai guba da ake fitarwa a duniya ne kadai nahiyar Afrika ke fitarwa, amma ita ce ta fi dandan kudarta sabili da matsalar.

  • Sin Ta Yi Tir Da Kalaman Karya Kan Dokar Tsaron Kasa Na HKSAR A Taron UNHRC

Yayin da ake ja-in-ja da manyan kasashe kan cika alkawarin da suka dauka na tallafawa kasashe masu tasowa musammam na Afrika wajen shawo kan matsalar yanayi, kasar Sin, wadda ita ma kasa ce mai tasowa, na ci gaba da bada gudunmuwarta ta duk wata kafa da ta san zai haifar da alfanu.

Yayin wani taron tattaunawa da aka yi a Nairobin Kenya a jiya, masana Sin da takwarorinsu na Afrika, sun jaddada kiran bunkasa tsare-tsaren noma masu dacewa da yanayi da kuma juriya, domin shawo kan matsalar yunwa.

Ba mutum abinci tallafi ne mai kyau, amma samar masa yadda zai samu abincin da kansa, ya fi kyautuwa. Don haka Sin bata tsaya ga tallafawa kasashen Afrika mabukata da abinci da kudi da ma kayayyaki ba, tana ci gaba da hobbasa wajen ganin sun samu hanyar samarwa kansu abinci da kansu, domin ba wannan ne karo na farko da masanan Sin ke zuwa nahiyar Afrika domin koyar da dabarun nom ana zamani ba.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Yunkurin masanan na lalubo hanyoyin inganta noma kamar a ko da yaushe, zai taimakwa gaya wajen shawo kan tarin matsalolin da ake fuskanta. Zai karawa manoma kwarin gwiwar dagewa wajen habaka aikin noma domin ciyar da al’umma wanda zai samar musu da karin kudin shiga da samar da karin guraben ayyukan yi.

Inganta tsare-tsaren noma za su taimaka gaya wajen kara jan hankalin matasa shiga harkar noma, lamarin da zai rage musu zaman kasha wando, da aikata muggan ayyuka tare da habaka tattallin arzikin kasashe. Idan muka yi nazari, wannan yunkuri idan ya tabbata, na iya shawo kan kusan dukkan matsalolin da nahiyar ke fuskanta, kamar yadda bahaushe kan ce, noma tushen arziki. Wannan ita ce mafita mai dorewa da za ta taimakawa nahiyar ba tare da ta tsaya jiran tsammani ba, domin wadancan manyan kasashe ba za su kawo mata daukin da ake fata ba.

Hakika kasar Sin na da gogewa a wannan fanni kasancewar bata da isasshen kasar noma, amma ita ke ciyar da al’ummarta har ma ta tallafawa wasu kasashen. Sin ta kasance aminiya ta kwarai mai kokarin lalubo hanyoyi masu dorewa na samun mafita ga kasashe masu tasowa, ba wai yin alkawari na fatar baki ba kadai ba. Kuma na san tabbas al’ummar Afrika sun san cewa kasar Sin da kamfanoni da masananta da ma jama’arta, su ne abokan hadin gwiwa na kwarai ba masu ci da guminsu ba.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bikin Sallah: Kungiyar CAN Ta Yi Kira Kan Hadin Kai, Zaman Lafiya, Soyayya  Domin Ci Gaban Nijeriya

Next Post

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Daga Landan Domin Bikin Babbar Sallah

Related

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

20 minutes ago
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

19 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

20 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

20 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

1 day ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

1 day ago
Next Post
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Daga Landan Domin Bikin Babbar Sallah

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Daga Landan Domin Bikin Babbar Sallah

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

June 8, 2025
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

June 8, 2025
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

June 8, 2025
Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

June 8, 2025
Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.