• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noma Tushen Arziki

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Noma Tushen Arziki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matsalar sauyin yanayi abu ne da a ko da yaushe ake ci gaba da tattaunawa kansa a duniya, domin lalubo bakin zaren warware mummunan tasirinta. A ci gaba da hakan ne, masana kimiyya na kasar Sin da na kasashen Afrika suka kira da a samo tsare-tsaren samar da abinci masu jure yanayi don kawar da yunwa a Afrika.

Kaso 2 zuwa 3 na hayaki mai guba da ake fitarwa a duniya ne kadai nahiyar Afrika ke fitarwa, amma ita ce ta fi dandan kudarta sabili da matsalar.

  • Sin Ta Yi Tir Da Kalaman Karya Kan Dokar Tsaron Kasa Na HKSAR A Taron UNHRC

Yayin da ake ja-in-ja da manyan kasashe kan cika alkawarin da suka dauka na tallafawa kasashe masu tasowa musammam na Afrika wajen shawo kan matsalar yanayi, kasar Sin, wadda ita ma kasa ce mai tasowa, na ci gaba da bada gudunmuwarta ta duk wata kafa da ta san zai haifar da alfanu.

Yayin wani taron tattaunawa da aka yi a Nairobin Kenya a jiya, masana Sin da takwarorinsu na Afrika, sun jaddada kiran bunkasa tsare-tsaren noma masu dacewa da yanayi da kuma juriya, domin shawo kan matsalar yunwa.

Ba mutum abinci tallafi ne mai kyau, amma samar masa yadda zai samu abincin da kansa, ya fi kyautuwa. Don haka Sin bata tsaya ga tallafawa kasashen Afrika mabukata da abinci da kudi da ma kayayyaki ba, tana ci gaba da hobbasa wajen ganin sun samu hanyar samarwa kansu abinci da kansu, domin ba wannan ne karo na farko da masanan Sin ke zuwa nahiyar Afrika domin koyar da dabarun nom ana zamani ba.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

Yunkurin masanan na lalubo hanyoyin inganta noma kamar a ko da yaushe, zai taimakwa gaya wajen shawo kan tarin matsalolin da ake fuskanta. Zai karawa manoma kwarin gwiwar dagewa wajen habaka aikin noma domin ciyar da al’umma wanda zai samar musu da karin kudin shiga da samar da karin guraben ayyukan yi.

Inganta tsare-tsaren noma za su taimaka gaya wajen kara jan hankalin matasa shiga harkar noma, lamarin da zai rage musu zaman kasha wando, da aikata muggan ayyuka tare da habaka tattallin arzikin kasashe. Idan muka yi nazari, wannan yunkuri idan ya tabbata, na iya shawo kan kusan dukkan matsalolin da nahiyar ke fuskanta, kamar yadda bahaushe kan ce, noma tushen arziki. Wannan ita ce mafita mai dorewa da za ta taimakawa nahiyar ba tare da ta tsaya jiran tsammani ba, domin wadancan manyan kasashe ba za su kawo mata daukin da ake fata ba.

Hakika kasar Sin na da gogewa a wannan fanni kasancewar bata da isasshen kasar noma, amma ita ke ciyar da al’ummarta har ma ta tallafawa wasu kasashen. Sin ta kasance aminiya ta kwarai mai kokarin lalubo hanyoyi masu dorewa na samun mafita ga kasashe masu tasowa, ba wai yin alkawari na fatar baki ba kadai ba. Kuma na san tabbas al’ummar Afrika sun san cewa kasar Sin da kamfanoni da masananta da ma jama’arta, su ne abokan hadin gwiwa na kwarai ba masu ci da guminsu ba.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bikin Sallah: Kungiyar CAN Ta Yi Kira Kan Hadin Kai, Zaman Lafiya, Soyayya  Domin Ci Gaban Nijeriya

Next Post

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Daga Landan Domin Bikin Babbar Sallah

Related

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali
Daga Birnin Sin

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

1 hour ago
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

1 hour ago
Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

20 hours ago
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi
Daga Birnin Sin

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

21 hours ago
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani
Daga Birnin Sin

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

22 hours ago
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha
Daga Birnin Sin

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

22 hours ago
Next Post
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Daga Landan Domin Bikin Babbar Sallah

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Daga Landan Domin Bikin Babbar Sallah

LABARAI MASU NASABA

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

May 10, 2025
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

May 10, 2025
Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

May 10, 2025
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

May 10, 2025
Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don YaÆ™i Da Ta’addanci

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don YaÆ™i Da Ta’addanci

May 10, 2025
Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

May 10, 2025
Noma

ECOWAS Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasar Tattalin Arzikin Afrika Ta Yamma – Kwamred Bishir Dauda

May 10, 2025
Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

Ƙungiyar Sadarwa Ta Ƙasa Ta Fitar da Sabbin Matakan Tallata Nasarorin Gwamnatin Tinubu

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.