• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noma Tushen Arziki

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Noma Tushen Arziki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Matsalar sauyin yanayi abu ne da a ko da yaushe ake ci gaba da tattaunawa kansa a duniya, domin lalubo bakin zaren warware mummunan tasirinta. A ci gaba da hakan ne, masana kimiyya na kasar Sin da na kasashen Afrika suka kira da a samo tsare-tsaren samar da abinci masu jure yanayi don kawar da yunwa a Afrika.

Kaso 2 zuwa 3 na hayaki mai guba da ake fitarwa a duniya ne kadai nahiyar Afrika ke fitarwa, amma ita ce ta fi dandan kudarta sabili da matsalar.

  • Sin Ta Yi Tir Da Kalaman Karya Kan Dokar Tsaron Kasa Na HKSAR A Taron UNHRC

Yayin da ake ja-in-ja da manyan kasashe kan cika alkawarin da suka dauka na tallafawa kasashe masu tasowa musammam na Afrika wajen shawo kan matsalar yanayi, kasar Sin, wadda ita ma kasa ce mai tasowa, na ci gaba da bada gudunmuwarta ta duk wata kafa da ta san zai haifar da alfanu.

Yayin wani taron tattaunawa da aka yi a Nairobin Kenya a jiya, masana Sin da takwarorinsu na Afrika, sun jaddada kiran bunkasa tsare-tsaren noma masu dacewa da yanayi da kuma juriya, domin shawo kan matsalar yunwa.

Ba mutum abinci tallafi ne mai kyau, amma samar masa yadda zai samu abincin da kansa, ya fi kyautuwa. Don haka Sin bata tsaya ga tallafawa kasashen Afrika mabukata da abinci da kudi da ma kayayyaki ba, tana ci gaba da hobbasa wajen ganin sun samu hanyar samarwa kansu abinci da kansu, domin ba wannan ne karo na farko da masanan Sin ke zuwa nahiyar Afrika domin koyar da dabarun nom ana zamani ba.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Yunkurin masanan na lalubo hanyoyin inganta noma kamar a ko da yaushe, zai taimakwa gaya wajen shawo kan tarin matsalolin da ake fuskanta. Zai karawa manoma kwarin gwiwar dagewa wajen habaka aikin noma domin ciyar da al’umma wanda zai samar musu da karin kudin shiga da samar da karin guraben ayyukan yi.

Inganta tsare-tsaren noma za su taimaka gaya wajen kara jan hankalin matasa shiga harkar noma, lamarin da zai rage musu zaman kasha wando, da aikata muggan ayyuka tare da habaka tattallin arzikin kasashe. Idan muka yi nazari, wannan yunkuri idan ya tabbata, na iya shawo kan kusan dukkan matsalolin da nahiyar ke fuskanta, kamar yadda bahaushe kan ce, noma tushen arziki. Wannan ita ce mafita mai dorewa da za ta taimakawa nahiyar ba tare da ta tsaya jiran tsammani ba, domin wadancan manyan kasashe ba za su kawo mata daukin da ake fata ba.

Hakika kasar Sin na da gogewa a wannan fanni kasancewar bata da isasshen kasar noma, amma ita ke ciyar da al’ummarta har ma ta tallafawa wasu kasashen. Sin ta kasance aminiya ta kwarai mai kokarin lalubo hanyoyi masu dorewa na samun mafita ga kasashe masu tasowa, ba wai yin alkawari na fatar baki ba kadai ba. Kuma na san tabbas al’ummar Afrika sun san cewa kasar Sin da kamfanoni da masananta da ma jama’arta, su ne abokan hadin gwiwa na kwarai ba masu ci da guminsu ba.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bikin Sallah: Kungiyar CAN Ta Yi Kira Kan Hadin Kai, Zaman Lafiya, Soyayya  Domin Ci Gaban Nijeriya

Next Post

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Daga Landan Domin Bikin Babbar Sallah

Related

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

15 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

15 hours ago
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II
Daga Birnin Sin

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

16 hours ago
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

18 hours ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

19 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

21 hours ago
Next Post
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Daga Landan Domin Bikin Babbar Sallah

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Daga Landan Domin Bikin Babbar Sallah

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

August 26, 2025
Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

August 26, 2025
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.