ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noma Tushen Arziki

by CMG Hausa
3 years ago
Noma

Matsalar sauyin yanayi abu ne da a ko da yaushe ake ci gaba da tattaunawa kansa a duniya, domin lalubo bakin zaren warware mummunan tasirinta. A ci gaba da hakan ne, masana kimiyya na kasar Sin da na kasashen Afrika suka kira da a samo tsare-tsaren samar da abinci masu jure yanayi don kawar da yunwa a Afrika.

Kaso 2 zuwa 3 na hayaki mai guba da ake fitarwa a duniya ne kadai nahiyar Afrika ke fitarwa, amma ita ce ta fi dandan kudarta sabili da matsalar.

  • Sin Ta Yi Tir Da Kalaman Karya Kan Dokar Tsaron Kasa Na HKSAR A Taron UNHRC

Yayin da ake ja-in-ja da manyan kasashe kan cika alkawarin da suka dauka na tallafawa kasashe masu tasowa musammam na Afrika wajen shawo kan matsalar yanayi, kasar Sin, wadda ita ma kasa ce mai tasowa, na ci gaba da bada gudunmuwarta ta duk wata kafa da ta san zai haifar da alfanu.

ADVERTISEMENT

Yayin wani taron tattaunawa da aka yi a Nairobin Kenya a jiya, masana Sin da takwarorinsu na Afrika, sun jaddada kiran bunkasa tsare-tsaren noma masu dacewa da yanayi da kuma juriya, domin shawo kan matsalar yunwa.

Ba mutum abinci tallafi ne mai kyau, amma samar masa yadda zai samu abincin da kansa, ya fi kyautuwa. Don haka Sin bata tsaya ga tallafawa kasashen Afrika mabukata da abinci da kudi da ma kayayyaki ba, tana ci gaba da hobbasa wajen ganin sun samu hanyar samarwa kansu abinci da kansu, domin ba wannan ne karo na farko da masanan Sin ke zuwa nahiyar Afrika domin koyar da dabarun nom ana zamani ba.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Yunkurin masanan na lalubo hanyoyin inganta noma kamar a ko da yaushe, zai taimakwa gaya wajen shawo kan tarin matsalolin da ake fuskanta. Zai karawa manoma kwarin gwiwar dagewa wajen habaka aikin noma domin ciyar da al’umma wanda zai samar musu da karin kudin shiga da samar da karin guraben ayyukan yi.

Inganta tsare-tsaren noma za su taimaka gaya wajen kara jan hankalin matasa shiga harkar noma, lamarin da zai rage musu zaman kasha wando, da aikata muggan ayyuka tare da habaka tattallin arzikin kasashe. Idan muka yi nazari, wannan yunkuri idan ya tabbata, na iya shawo kan kusan dukkan matsalolin da nahiyar ke fuskanta, kamar yadda bahaushe kan ce, noma tushen arziki. Wannan ita ce mafita mai dorewa da za ta taimakawa nahiyar ba tare da ta tsaya jiran tsammani ba, domin wadancan manyan kasashe ba za su kawo mata daukin da ake fata ba.

Hakika kasar Sin na da gogewa a wannan fanni kasancewar bata da isasshen kasar noma, amma ita ke ciyar da al’ummarta har ma ta tallafawa wasu kasashen. Sin ta kasance aminiya ta kwarai mai kokarin lalubo hanyoyi masu dorewa na samun mafita ga kasashe masu tasowa, ba wai yin alkawari na fatar baki ba kadai ba. Kuma na san tabbas al’ummar Afrika sun san cewa kasar Sin da kamfanoni da masananta da ma jama’arta, su ne abokan hadin gwiwa na kwarai ba masu ci da guminsu ba.

 

Noma
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Daga Landan Domin Bikin Babbar Sallah

Tinubu Ya Dawo Nijeriya Daga Landan Domin Bikin Babbar Sallah

LABARAI MASU NASABA

Noma

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Noma

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.