• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NSCDC Ta Yaye Dakaru Na Musamman A Zamfara

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
NSCDC Ta Yaye Dakaru Na Musamman A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A fadi-tashin da yake yi wajen samar da ingataccen tsaro, Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada kudirin gwamnatin sa na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyar al’ummar Jihar Zamfara.

A ranar Talatar nan ne gwamnan ya halarci bikin yaye wasu dakaru na musamman, wadanda ke karkarshin Hukumar tsaro ta Sibil Difens (NSCDC) da ake kira ‘Agro Rangers’ a Jihar Zamfara.

  • Sin Ta Kiyaye Zaman Lafiya Da Tsaron Kasa Da Kasa Bisa Ayyukanta Masu Amfani
  • Sirrin Zaman Lafiyar Da Ake Mora A Jihar Nasarawa –Kakakin Gwamnan Jihar

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa, dakarun na ‘Agro Rangers’, jami’ai ne na musamman a Hukumar ta Sibil Difens, wadanda suka samu horo mai zurfi.

Ya kuma kara da cewa, an horar da jami’an na musamman a shirye-shiryen gudanar da aikin hadin gwiwa a yaki da ’yan bindiga a Jihar Zamfara.

A yayin jawabinsa a wajen bikin, gwamna Lawal ya yaba wa hukumar NSCDC bisa wannan shiri nasu. Ya ce, “Wannan ya zo ne a wani muhimmin lokaci kuma ya yi daidai da kudurinmu na daukar ingantattun matakan yaki da rashin tsaro.

Labarai Masu Nasaba

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

“Mun dauki wannan a matsayin babban mataki na tunkarar kalubalen da ya kawo cikas ga al’ummar mu wajen ayyukan noma, sana’o’in dogaro da kai, da sauran hanyoyin sa-mar da abinci a jihar.

“Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana harkokin tsaro da noma a matsayin muhimman abubuwan da suka sa a gaba. Mun bullo da matakai daban-daban don magance kalu-balen tsaro da kuma bunkasa noma a jihar. Don haka, muna kallon wannan shiri na ja-mi’an Hukumar Sibil Difens a matsayin wani gagarumin mataki na ci gaba da daukar matakan tsaro da muke dauka a matsayin gwamnati tare da jami’an tsaro da ke aiki a jihar.

“A matsayinmu na gwamnati, za mu ci gaba da bada hadin kai da cibiyoyi, kungiyoyi da daidaikun mutane wajen yaki da duk wani nau’in miyagun laifuka. Mun himmatu wajen samar da tallafin da wadannan cibiyoyi da daidaikun mutane ke bukata don gudanar da ayyukansu. Manufar farko ita ce tabbatar da tsaron al’ummominmu da kuma sanya su cikin aminci don ayyukan zamantakewa da tattalin arziki wanda zai saukake ci gaban jihar da jama’a.

“Ina matukar fatan shirin hukumar NSCDC na samar da wani dakarun na musamman, wanda hakan zai samar da mafita mai dorewa ga kalubalen tsaro da ake fuskanta, mu-samman wadanda suka shafi harkar noma.

“Ina da alfahari da kaddamar da wannan dakaru. Ina yi muku fatan alheri bisa sauke nauyin da aka dora muku. Ina rokon Allah Ya tsare ku, sannan Ya yi muku jagoranci.”

Tun da farko, Kwamandan Rundunar Sibil Difens a Jihar Zamfara, Kwamanda Sani Mustapha, ya gode wa Gwamna Lawal da gwamnatin Jihar bisa tallafin da suka ba shirin horarwa da dakarun Agro Rangers.

“Yallabai, dimbin goyon bayan da ka ke baiwa rundunar ta sa muka kai ga haka. Muna godiya kwarai da gaske,” inji shi.

Kwamandan ya kara da cewa, Hukumar ta NSCDC ta himmatu wajen samar da zaman lafiya da magance rikice-rikice a yankunan da ake fama da rikici.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NSCDCPoliceSecurity
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsoho Mai Shekara 70 Ya Shiga Hannu Kan Safarar Wiwi

Next Post

Tsarin Tazarar Haihuwa Mara Amfani Da Magani (2)

Related

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

22 minutes ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

26 minutes ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

1 hour ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

4 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

6 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

20 hours ago
Next Post
Tsarin Tazarar Haihuwa Mara Amfani Da Magani (2)

Tsarin Tazarar Haihuwa Mara Amfani Da Magani (2)

LABARAI MASU NASABA

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.