• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NUJ Ta Yi Allah Wadai Da Kama ‘Yan Jarida A Abuja

by Khalid Idris Doya
3 years ago
NUJ

Reshen birnin tarayya (FCT) na kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ), ta yi tir da da Allawadai da kamawa da tsare Edita Mista Ediri Oyibo da Paul Utebor dan rahoton kafar yada labarai ta yanar gizo, TheNewsGuru.com.

Jami’an ‘yansandan shiyya ta 7 da ke babban birnin tarayya Abuja ce ta cafke su.

  • NUJ Kebbi Ta Yi Alhini Rasuwar Tsohon dan Jarida Ibrahim Argungu

A wata sanarwar manema labarai da shugaban NUJ a FCT, Mista Emmanuel Ogbeche ya fitar, ya misalta kamen da aka yi wa ‘yan jarida abun da ba za a lamunta ba kuma kamene da aka yi ba tare da amfani da hankali ba.

A cewarsa, an aike da wasikar gayyata ga Oyibo da Utebo domin yin hira da mataimakin kwamishinan ‘yansanda (DCP), da ke kula da sashin binciken manyan laifuka (CID), wasikar mai dauke da kwanan wata 18 ga watan Fabrairun 2023 amma daga bisani kawai aka cafkesu bayan zuwansu.

Ya ce, “Yansandan sun yi ikirarin a cikin wasikar cewa suna binciken wani kes ne na hada baki, bata suna, bada bayanai na karya da barazana kan rayuwa ga su ‘yan jaridan kan labarin haihuwar wani yaro.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

“Zuwan ‘yan jaridan ke da wuya ne ‘yansandan suka kama ‘yan jarida kan wani takardar korafi da Adaobi Alagwu da cewa sun wallafa wani labari da ke cewa tsohowar shugaban bankin Skye, Tunde Ayeni ta karyata yi zargin cewa ba ita ce ta haifi danta ba.

“Yan jaridan, wadanda suka shafe tsawon kwanaki hudu a tsare cikin yanayi marar kyau, sannan an ki bada belinsu ba duk da ganawa da aka yi ta yi, sannan an nemi su kawo ma’aikacin gwamnati mai matakin aiki da bai yi kasa da level 14 a matsayin mai tsaya musu ba.

“Abun mamaki, bayan cika sharadin belin, a ranar Juma’a ga watan Fabrairun 24, cikin gaggawa ‘yansandan suka je suka gurfanar da su a gaban kotun majistire a cikin FCT da ke Wuse Zone 6 amma sun samu kotun ba zauna ba. Amma ‘yansandan sun cigaba da tsaresu ta haramtaccen hanya.

“NUJ tana bukatar a gaggauta sake Mr. Ediri Oyibo da Paul Utebor sannan muna neman ‘yansada su cigaba da bin hanyoyin da suka dace wajen gudanar da ayyukan da ke gabansu.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri
Labarai

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar
Manyan Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Next Post
Jam’iyyar NNPP Mai Kayan Marmari Na Shirin Yi Wa APC Fafalolo A Kano

Jam'iyyar NNPP Mai Kayan Marmari Na Shirin Yi Wa APC Fafalolo A Kano

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

Gwamnatin Katsina Ta Ƙara Samar Da Dakarun Tsaro 200 Domin Maganace Ta’addanci

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.