• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ofishin Fansho Na Jihar Kaduna Zai Fara Tantance Tsoffin Ma’aikatan Jihar A Ranar Laraba

by Sulaiman
2 years ago
Fansho

Ofishin da ke kula da ‘yan fasho na jihar Kaduna karkashin jagorancin Farfesa Salamatu Idris Isah, ya bayyana cewa, Ofishin ya fitar da sunayen wadanda za su ci gajiyar shirin, inda za a fara tantance su a shiyyoyi Uku da ke fadin jihar.

Farfesa ta bayyana hakan ne a ranar Alhamis a ofishinta yayin da ta ke zantawa da manema labarai kan shirin fara tantance ma’aikatan da za su ci gajiyar shirin.

  • Mutane 195 Isra’ila Ta Kashe A Harin Sansanin Jabalia Da Ke Gaza
  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Cikakken ‘Yancin Kan Kasar Sudan

Don haka, wadanda ke cikin shiyya ta biyu (kwaryar jihar Kaduna) za a tantance su a ofishin kula da ‘yan fashon da ke Katuru Road, Badarawa GRA, inda za a fara aikin tantancewar a fadin jihar baki daya a ranar 8 zuwa 15 ga watan Nuwamba, 2023.

Wadanda aka tantancen za su fara jin makudan kudadensu a asusun ajiyarsu na banki daga ranar 18 ga watan Nuwamban.

Tsarin biyan, an kasa shi ne zuwa tsoho da sabon tsari: a karkashin tsohon tsari a bangaren ma’aikatan jiha, wannan shi ne rukuni na 22 yayin da a bangaren ma’aikatan kananan hukumomi ya kasance rukuni na 20. A bangaren sabon tsari, wannan shi ne rukuni na 51.

LABARAI MASU NASABA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Farfesa ta kara da cewa, ofishin ya shirya biyan tsoffin ma’aikatan 1,051 inda aka ware tsoffin ma’aikata a tsohon tsari na jiha 331, sannan na kananan hukumomi su 542. A sabon tsari, an ware tsoffin ma’aikatan su 178.

Bugu da kari, hukumar ta kasafta kudin da gwamnan ya fitar zuwa gida biyu, inda aka ware Naira Biliyan N2,600,000 don biyan tsoffin ma’aikatan da ke kan tsohon tsarin, ragowar Naira Miliyan N500,000 aka sanya shi don biyan tsoffin ma’aikatan da ke kan sabon tsari.

Farfesa, da take amsa tambaya kan masu korafin cewa, ba su ga sunansu ba, ta ce, “su yi hakuri ba a zo kansu ba ne, sunayen a tsare suke, ba a tsallake, don haka, ba za a tsallake kowa ba.”

A karshe ta yi gargadi ga masu cin gajiyar shirin kan cewa, Hukumar bata nada kowa ba kan ya amsa sisi ko kobo da nufin shiga tsarin amsar kudin fansho da garatuti, “hakkinku ne kuma dole a baku.”

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma
Labarai

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA'A

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.