• English
  • Business News
Monday, November 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ofishin Jakadancin Saudiyya Ya Yi Bikin Cikar Daularsu Shekaru 94 Tare Da Karfafa Alaka Da Nijeriya

by Abdulrazaq Yahuza and Sulaiman
1 year ago
Saudiyya

Ofishin Jakadancin Saudiyya da ke Abuja ya gudanar da bikin tunawa da ranar kafa kasar ta Saudiyya karo na 94 a gidan jakadan kasar, Faisal bin Ebraheem Alghamdi.

 

Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, shugabannin ofisoshin diflomasiyya, wakilan kungiyoyin duniya da sauran manyan ‘yan kasuwa.

  • Tarihin Ci Gaban Sin: Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Ƴan Ta’adda Sun Lalata Wutar Lantarkin Maiduguri Zuwa Damaturu

Da yake jawabi, Ambasada Alghamdi ya bayyana muhimmancin bikin, wanda ke nuna cika shekaru 94 da kafa Daular kasar ta Sarki Abdulaziz bin Abdulrahman Al Saud, wacce ta yi tsayin daka bisa tsarin akidar Musulunci da kiyaye dabi’u na daidaito, adalci, da amana.

 

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Ya jaddada cewa, Masarautar Saudiyya ita ce ta farko a cikin daulolin da aka kafa a yankin Gabas ta Tsakiya wacce ta zamo abin koyi, inda hakan ke nuni da irin ci gaban da ta samu.

 

Ambasada Alghamdi ya kuma yi amfani da damar wajen nuna farin ciki da dadaddiyar alakar da ke tsakanin Saudiyya da Nijeriya, wadda take samun ci gaba tun bayan kafuwarta sama da shekaru 63.

Saudiyya

Bugu da kari, Ambasada Alghamdi ya bayyana jajircewar Saudiyya wajen tabbatar da annashuwa da kwanciyar hankalin mahajjata da masu Umurah, inda a shekarar 2023, Masarautar ta bai wa ‘Yan Nijeriya 120,000 damar zuwa aikin Umrah da kuma masu zuwa aikin Hajji su 65,000.

 

Bugu da kari, Jakadan ya bayyana cewa, Masarautar Saudiyya ta bayar da tallafin karatu ga daliban Nijeriya maza da mata 260, wanda hakan ya kara habaka musayar ilimi a tsakanin kasashen biyu. Ya kuma bayyana cewa, yawan cinikin da ke tsakanin Saudiyya da Nijeriya ya habaka zuwa dala miliyan 600.

 

Ambasada Alghamdi ya kuma tabo zancen ayyukan jin kai da Masarautar take yi a Nijeriya, ciki har da aikin sa kai na Nur-Saudi wanda kashi na farko ya mayar da hankali a kan magance cutar makanta da yoyon fitsari da kuma ciwon zuciya.

 

“Daya daga cikin muhimman abubuwan da Masarautar ta samu a fannin jinya a Nijeriya shi ne nasarar raba wasu tagwayen Nijeriya da aka yi a watan Mayu, wanda hakan wani muhimmin ci gaba ne a bangaren likitocin Saudiyya.

Saudiyya

“Wannan tiyatar ita ce tiyatar raba mutane ta 56 wadda likitocin Saudiyya suka yi, kuma har yanzu kasar Saudiyya na daya daga cikin manyan kasashen duniya wajen gudanar da irin wadannan ayyuka masu sarkakiya.” In ji shi.

 

Jakadan ya kuma yi karin haske kan burin Saudiyya na 2030, da shirin kawo sauyi na duniya da ke neman samar da al’umma mai alfanu, da gina tattalin arziki da kuma qasa mai kishi.

 

Ambasada Alghamdi ya tabbatar da cewa Masarautar kasarsu ta himmatu wajen samar da damammaki ga ‘yan kasarta da abokan huldarta na duniya ciki har da Nijeriya, ta wannan hanya ta hangen nesa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Sin Ta Samu Karuwar Mazauna Birane Cikin Shekaru 75

Sin Ta Samu Karuwar Mazauna Birane Cikin Shekaru 75

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Ci Gaba Da Zama Muhimmin Ginshiki Ga Ci Gaban Nahiyar 

November 9, 2025
An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.