ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ofishin Jakadancin Saudiyya Ya Yi Bikin Cikar Daularsu Shekaru 94 Tare Da Karfafa Alaka Da Nijeriya

by Abdulrazaq Yahuza and Sulaiman
2 years ago
Saudiyya

Ofishin Jakadancin Saudiyya da ke Abuja ya gudanar da bikin tunawa da ranar kafa kasar ta Saudiyya karo na 94 a gidan jakadan kasar, Faisal bin Ebraheem Alghamdi.

 

Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, shugabannin ofisoshin diflomasiyya, wakilan kungiyoyin duniya da sauran manyan ‘yan kasuwa.

ADVERTISEMENT
  • Tarihin Ci Gaban Sin: Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Ƴan Ta’adda Sun Lalata Wutar Lantarkin Maiduguri Zuwa Damaturu

Da yake jawabi, Ambasada Alghamdi ya bayyana muhimmancin bikin, wanda ke nuna cika shekaru 94 da kafa Daular kasar ta Sarki Abdulaziz bin Abdulrahman Al Saud, wacce ta yi tsayin daka bisa tsarin akidar Musulunci da kiyaye dabi’u na daidaito, adalci, da amana.

 

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Ya jaddada cewa, Masarautar Saudiyya ita ce ta farko a cikin daulolin da aka kafa a yankin Gabas ta Tsakiya wacce ta zamo abin koyi, inda hakan ke nuni da irin ci gaban da ta samu.

 

Ambasada Alghamdi ya kuma yi amfani da damar wajen nuna farin ciki da dadaddiyar alakar da ke tsakanin Saudiyya da Nijeriya, wadda take samun ci gaba tun bayan kafuwarta sama da shekaru 63.

Saudiyya

Bugu da kari, Ambasada Alghamdi ya bayyana jajircewar Saudiyya wajen tabbatar da annashuwa da kwanciyar hankalin mahajjata da masu Umurah, inda a shekarar 2023, Masarautar ta bai wa ‘Yan Nijeriya 120,000 damar zuwa aikin Umrah da kuma masu zuwa aikin Hajji su 65,000.

 

Bugu da kari, Jakadan ya bayyana cewa, Masarautar Saudiyya ta bayar da tallafin karatu ga daliban Nijeriya maza da mata 260, wanda hakan ya kara habaka musayar ilimi a tsakanin kasashen biyu. Ya kuma bayyana cewa, yawan cinikin da ke tsakanin Saudiyya da Nijeriya ya habaka zuwa dala miliyan 600.

 

Ambasada Alghamdi ya kuma tabo zancen ayyukan jin kai da Masarautar take yi a Nijeriya, ciki har da aikin sa kai na Nur-Saudi wanda kashi na farko ya mayar da hankali a kan magance cutar makanta da yoyon fitsari da kuma ciwon zuciya.

 

“Daya daga cikin muhimman abubuwan da Masarautar ta samu a fannin jinya a Nijeriya shi ne nasarar raba wasu tagwayen Nijeriya da aka yi a watan Mayu, wanda hakan wani muhimmin ci gaba ne a bangaren likitocin Saudiyya.

Saudiyya

“Wannan tiyatar ita ce tiyatar raba mutane ta 56 wadda likitocin Saudiyya suka yi, kuma har yanzu kasar Saudiyya na daya daga cikin manyan kasashen duniya wajen gudanar da irin wadannan ayyuka masu sarkakiya.” In ji shi.

 

Jakadan ya kuma yi karin haske kan burin Saudiyya na 2030, da shirin kawo sauyi na duniya da ke neman samar da al’umma mai alfanu, da gina tattalin arziki da kuma qasa mai kishi.

 

Ambasada Alghamdi ya tabbatar da cewa Masarautar kasarsu ta himmatu wajen samar da damammaki ga ‘yan kasarta da abokan huldarta na duniya ciki har da Nijeriya, ta wannan hanya ta hangen nesa.

Saudiyya
Abdulrazaq Yahuza
+ posts Bio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya
Saudiyya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Sin Ta Samu Karuwar Mazauna Birane Cikin Shekaru 75

Sin Ta Samu Karuwar Mazauna Birane Cikin Shekaru 75

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.