• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ofishin Jakadancin Saudiyya Ya Yi Bikin Cikar Daularsu Shekaru 94 Tare Da Karfafa Alaka Da Nijeriya

by Abdulrazaq Yahuza and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Ofishin Jakadancin Saudiyya Ya Yi Bikin Cikar Daularsu Shekaru 94 Tare Da Karfafa Alaka Da Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ofishin Jakadancin Saudiyya da ke Abuja ya gudanar da bikin tunawa da ranar kafa kasar ta Saudiyya karo na 94 a gidan jakadan kasar, Faisal bin Ebraheem Alghamdi.

 

Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, shugabannin ofisoshin diflomasiyya, wakilan kungiyoyin duniya da sauran manyan ‘yan kasuwa.

  • Tarihin Ci Gaban Sin: Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Ƴan Ta’adda Sun Lalata Wutar Lantarkin Maiduguri Zuwa Damaturu

Da yake jawabi, Ambasada Alghamdi ya bayyana muhimmancin bikin, wanda ke nuna cika shekaru 94 da kafa Daular kasar ta Sarki Abdulaziz bin Abdulrahman Al Saud, wacce ta yi tsayin daka bisa tsarin akidar Musulunci da kiyaye dabi’u na daidaito, adalci, da amana.

 

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

‘Yansanda Sun Kuɓutar Da ‘Yan Ghana 19 Da Aka Yaudare Su Zuwa Nijeriya

Ya jaddada cewa, Masarautar Saudiyya ita ce ta farko a cikin daulolin da aka kafa a yankin Gabas ta Tsakiya wacce ta zamo abin koyi, inda hakan ke nuni da irin ci gaban da ta samu.

 

Ambasada Alghamdi ya kuma yi amfani da damar wajen nuna farin ciki da dadaddiyar alakar da ke tsakanin Saudiyya da Nijeriya, wadda take samun ci gaba tun bayan kafuwarta sama da shekaru 63.

Saudiyya

Bugu da kari, Ambasada Alghamdi ya bayyana jajircewar Saudiyya wajen tabbatar da annashuwa da kwanciyar hankalin mahajjata da masu Umurah, inda a shekarar 2023, Masarautar ta bai wa ‘Yan Nijeriya 120,000 damar zuwa aikin Umrah da kuma masu zuwa aikin Hajji su 65,000.

 

Bugu da kari, Jakadan ya bayyana cewa, Masarautar Saudiyya ta bayar da tallafin karatu ga daliban Nijeriya maza da mata 260, wanda hakan ya kara habaka musayar ilimi a tsakanin kasashen biyu. Ya kuma bayyana cewa, yawan cinikin da ke tsakanin Saudiyya da Nijeriya ya habaka zuwa dala miliyan 600.

 

Ambasada Alghamdi ya kuma tabo zancen ayyukan jin kai da Masarautar take yi a Nijeriya, ciki har da aikin sa kai na Nur-Saudi wanda kashi na farko ya mayar da hankali a kan magance cutar makanta da yoyon fitsari da kuma ciwon zuciya.

 

“Daya daga cikin muhimman abubuwan da Masarautar ta samu a fannin jinya a Nijeriya shi ne nasarar raba wasu tagwayen Nijeriya da aka yi a watan Mayu, wanda hakan wani muhimmin ci gaba ne a bangaren likitocin Saudiyya.

Saudiyya

“Wannan tiyatar ita ce tiyatar raba mutane ta 56 wadda likitocin Saudiyya suka yi, kuma har yanzu kasar Saudiyya na daya daga cikin manyan kasashen duniya wajen gudanar da irin wadannan ayyuka masu sarkakiya.” In ji shi.

 

Jakadan ya kuma yi karin haske kan burin Saudiyya na 2030, da shirin kawo sauyi na duniya da ke neman samar da al’umma mai alfanu, da gina tattalin arziki da kuma qasa mai kishi.

 

Ambasada Alghamdi ya tabbatar da cewa Masarautar kasarsu ta himmatu wajen samar da damammaki ga ‘yan kasarta da abokan huldarta na duniya ciki har da Nijeriya, ta wannan hanya ta hangen nesa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tarihin Ci Gaban Sin: Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Next Post

Sin Ta Samu Karuwar Mazauna Birane Cikin Shekaru 75

Related

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
Manyan Labarai

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

40 minutes ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Labarai

‘Yansanda Sun Kuɓutar Da ‘Yan Ghana 19 Da Aka Yaudare Su Zuwa Nijeriya

2 hours ago
ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

4 hours ago
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hallaka ‘Yan Sa-kai Sama Da 70 A Filato

4 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

5 hours ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Manyan Labarai

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

6 hours ago
Next Post
Sin Ta Samu Karuwar Mazauna Birane Cikin Shekaru 75

Sin Ta Samu Karuwar Mazauna Birane Cikin Shekaru 75

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

July 8, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kuɓutar Da ‘Yan Ghana 19 Da Aka Yaudare Su Zuwa Nijeriya

July 8, 2025
ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

July 8, 2025
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

‘Yan Bindiga Sun Hallaka ‘Yan Sa-kai Sama Da 70 A Filato

July 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

July 8, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.