• English
  • Business News
Monday, September 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ofishin Jakadancin Sin Dake Najeriya Ya Gudanar Da Liyafar Murnar Cika Shekaru 75 Da Kafuwar Sabuwar Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ofishin Jakadancin Sin Dake Najeriya Ya Gudanar Da Liyafar Murnar Cika Shekaru 75 Da Kafuwar Sabuwar Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ofishin jakadancin Sin dake Najeriya ya gudanar da liyafar murnar cika shekaru 75 da kafuwar sabuwar kasar Sin, jakadan Sin dake kasar Yu Dunhai da shugaban majalisar wakilan Najeriya Abbas Tajudeen sun halarci bikin tare da gabatar da jawabai.

 

Jakada Yu ya waiwayi ci gaban da Sin ta samu a cikin wadannan shekaru 75 da suka gabata, kuma ya ce, wannan shi ne karo na da shugaban kasar Najeriya Bola Tinubu ya kai ziyarar aiki a kasar Sin bayan hawa karagar mulki, da ma halartar taron kolin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika, inda shugabanin kasashen biyu sun kai ga matsaya daya wajen daga huldar kasashen biyu zuwa dangantakar abota bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni, matakin da ya bude sabon babi na raya huldarsu. Ban da wannan kuma, bangarorin biyu sun kulla yarjejeniyoyin hadin gwiwa fiye da 10, don tabbatar da yin ingantaccen hadin gwiwa karkashin shawarar “ziri daya da hanya daya”.

  • Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin
  • Gwamnan Kano Ya Nada Hauwa Isah Ibrahim Manajan Daraktan ARTV

A nasa bangare, Tajudeen ya taya Yu murnar zama sabon jakadan Sin dake Najeriya, ya ce, sabuwar kasar Sin na samun bunkasuwa mai armashi a bangaren tattalin arziki da kimiya da fasaha da ma al’umma, tun kafuwarta a shekarar 1949, Sin kasa ce dake samun saurin bunkasuwa kuma jigon duniya wajen yin kwaskwarima, kuma karfinta na kara bayyanawa wajen dunkulewar duniya baki daya.

Tajudeen ya kara da cewa, Sin da Najeriya na zurfafa huldarsu bisa tushen mutunta juna. A gun taron koli na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka da aka gudanar ba da dadewa ba, yarjejeniyoyin da shugabanin kasashen biyu suka kulla a gun taron, sun jaddada niyyar kasashen biyu na zurfafa huldarsu, wadanda suka samar da nagartacciyar hanya ga Najeriya wajen samun jari a wasu muhimman bangarori ciki har da samar da makamashi da kimiyya da sauransu. Majalisarsa za ta tsai da wasu dokoki don nuna goyon baya ga kokarin tabbatar da ci gaban da shugabanin suka samu a yayin taron. (Amina Xu)

Labarai Masu Nasaba

Za A Gudanar Da Bikin Ajiye Furanni Don Jinjinawa Jarumai A Ranar 30 Ga Satumba

Ana Hasashen Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Yayin Hutun Bikin Tsakiyar Kaka Na Sin Zai Kai Biliyan 2.36


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci gaban tattalin arzikin SinJapanSib
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

Next Post

Birtaniya Ta Bukaci ‘Yan Kasarta Su Gaggauta Ficewa Daga Lebanon

Related

Za A Gudanar Da Bikin Ajiye Furanni Don Jinjinawa Jarumai A Ranar 30 Ga Satumba
Daga Birnin Sin

Za A Gudanar Da Bikin Ajiye Furanni Don Jinjinawa Jarumai A Ranar 30 Ga Satumba

14 hours ago
Ana Hasashen Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Yayin Hutun Bikin Tsakiyar Kaka Na Sin Zai Kai Biliyan 2.36
Daga Birnin Sin

Ana Hasashen Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Yayin Hutun Bikin Tsakiyar Kaka Na Sin Zai Kai Biliyan 2.36

15 hours ago
Kwararrun Afirka Sun Jinjinawa Hadin Gwiwar Kirkire-Kirkire Tsakanin Kasashen Nahiyar Da Sin
Daga Birnin Sin

Kwararrun Afirka Sun Jinjinawa Hadin Gwiwar Kirkire-Kirkire Tsakanin Kasashen Nahiyar Da Sin

16 hours ago
CMG Ya Yi Ayyukan Hadin Gwiwa Da Bangarori Daban Daban Na Macao
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Ayyukan Hadin Gwiwa Da Bangarori Daban Daban Na Macao

17 hours ago
Xi Ya Yi Kira Ga Makarantun Horar Da ‘Yan Jam’iyya Da Su Kara Azamar Kyankyashe Hazikai Da Gabatar Da Shawarwari Ga JKS
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Makarantun Horar Da ‘Yan Jam’iyya Da Su Kara Azamar Kyankyashe Hazikai Da Gabatar Da Shawarwari Ga JKS

18 hours ago
Ofishin Jakadancin Sin a Nijar Ya Shirya Liyafar Bikin Murnar Cika Shekaru 76 Da Kafa Jamhuriyar Jama’ar Sin
Daga Birnin Sin

Ofishin Jakadancin Sin a Nijar Ya Shirya Liyafar Bikin Murnar Cika Shekaru 76 Da Kafa Jamhuriyar Jama’ar Sin

19 hours ago
Next Post
Sin

Birtaniya Ta Bukaci ‘Yan Kasarta Su Gaggauta Ficewa Daga Lebanon

LABARAI MASU NASABA

Jirgin Ƙasan Abuja–Kaduna Zai Dawo Aiki 1 Ga Oktoba – NRC

Jirgin Ƙasan Abuja–Kaduna Zai Dawo Aiki 1 Ga Oktoba – NRC

September 29, 2025
Barcelona Ta Ɗare Kan Teburin Laliga Bayan Doke Real Sociedad

Barcelona Ta Ɗare Kan Teburin Laliga Bayan Doke Real Sociedad

September 29, 2025
Rikicin Dangote Da PENGASSAN Ba Zai Kawo Wahalar Fetur Ba

Rikicin Dangote Da PENGASSAN Ba Zai Kawo Wahalar Fetur Ba

September 29, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sallami Kwamishinar Mata Daga Aiki

Gwamnan Bauchi Ya Sallami Kwamishinar Mata Daga Aiki

September 29, 2025
Za A Gudanar Da Bikin Ajiye Furanni Don Jinjinawa Jarumai A Ranar 30 Ga Satumba

Za A Gudanar Da Bikin Ajiye Furanni Don Jinjinawa Jarumai A Ranar 30 Ga Satumba

September 28, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Dagacin Ogbayo Da Jami’an Ƴan Sa-Kai 11 A Kwara

Ƴan Bindiga Sun Kashe Dagacin Ogbayo Da Jami’an Ƴan Sa-Kai 11 A Kwara

September 28, 2025
Ana Hasashen Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Yayin Hutun Bikin Tsakiyar Kaka Na Sin Zai Kai Biliyan 2.36

Ana Hasashen Adadin Zirga-Zirgar Fasinjoji Yayin Hutun Bikin Tsakiyar Kaka Na Sin Zai Kai Biliyan 2.36

September 28, 2025
Firimiyar Nijeriya: Barau FC Ta Samu Nasarar Farko A Tarihinta

Firimiyar Nijeriya: Barau FC Ta Samu Nasarar Farko A Tarihinta

September 28, 2025
Kwararrun Afirka Sun Jinjinawa Hadin Gwiwar Kirkire-Kirkire Tsakanin Kasashen Nahiyar Da Sin

Kwararrun Afirka Sun Jinjinawa Hadin Gwiwar Kirkire-Kirkire Tsakanin Kasashen Nahiyar Da Sin

September 28, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 14 A Borno Da Adamawa, Sun Ƙwato Makamai

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 14 A Borno Da Adamawa, Sun Ƙwato Makamai

September 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.