• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ohanaeze Ta Bukaci Tinubu Ya Saki Nnamdi Kanu Idan Aka Rantsar Da Shi

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Ohanaeze Ta Bukaci Tinubu Ya Saki Nnamdi Kanu Idan Aka Rantsar Da Shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da Nijeriya ke kara kusantar ranar 29 ga watan Mayu, da za a rantsar da zababben shugaba kasa, kungiyar Ohanaeze Ndigbo, ta fitar da wasu bukatu hudu da ta ke so Bola Tinubu, ya cika domin kwantar da hankalin ‘yan kabilar Igbo.

Babban Sakataren kungiyar Ohanaeze, Okechukwu Isiguzoro, ya ce ya kamata Tinubu ya saki Nnamdi Kanu, shugaban masu fafutukar kafa kasar Biyafra (IPOB), ba tare da wani sharadi ba.

  • Sin: Fannin Sayayya Da Na Yawon Shakatawa Na Kara Farfadowa A Rubu’in Farko Na Bana
  • Gwamnatin Kaduna Ta Sassauta Dokar Zirga-Zirga Da Ta Saka A Wasu Yankuna

Isiguzoro, ya ce sakin Kanu zai dawo da zaman lafiya da tsaro a yankin Kudu maso Gabashin kasar nan.

Ya yi nuni da cewa, dole ne Tinubu ya tabbatar da yankin Kudu maso Gabas ya samar da shugaban majalisar dattawa.

Jigon na Ohanaeze, ya ce dole ne Tinubu ya tabbatar da ganin an kirkiri jiha ta shida a yankin kudu maso Gabas.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

A cewar Isiguzoro: “Tinubu mai son ci gaba ne, shi mai dabara ne; gwamnatin Tinubu ba za ta zama kamar gwamnatin Buhari ba.

“Matsalar Tinubu, ita ce yawan shekaru, da kuma mafi yawan mutanen da suka sa Buhari bai yi nasara ba suna bayansa saboda wasu kalubalen da ya ke fuskanta biyo bayan zaben 2023.

“Dole ne Tinubu ya tabbatar wa da yankin Kudu maso Gabas wadannan muhimman bukatu hudu don yankin ya amince da shi a matsayin shugaban Nijeriya, kana kabilar Igbo su tsaya tsayin-daka su kare mulkinsa.

“Na farko shi ne, dole ne Tinubu ya maido da zaman lafiya da tsaro ba tare da wani sharadi ba ta hanyar sakin Nnamdi Kanu, ko zai ba shi afuwar shugaban kasa a lokacin jawabin karbar mulkinsa ko kuma ya yi amfani da karfin ikon shugaban kasa wajen ganin an sake shi domin dawo da zaman lafiya da tsaro a yankin kudu maso gabas.

“Na biyu, dole ne Tinubu ya fara aikin warkarwa wurin ganin ya daidaita tikitin Musulmi da Musulmi a takarar shugaban kasa ta hanyar bai wa Kirista daga Kudu maso Gabas shugaban majalisar dattawa. Duk wanda zai zama Shugaban Majalisar Dattawa ka da ya zama wani Sanata mai mukami a majalisar wadanda ba shi da kishin kasa.

“Muna kira ga majalisar dattawa da ta gyara dokokinta tare da ba da izinin sababbin ‘yan majalisa su jagorancin majalisar saboda Sanatocin da ke rike da mukamin akwai shakku a kan su kuma ba za su iya kare muradun Ndigbos (kabilar Igbo) ba.

“Na uku, dole ne Tinubu ya sanya tsarin siyasa da zai tabbatar da cewa ‘yan kabilar Igbo sun ga alkawarin da Buhari ya yi masu a asirce cewa zai tabbatar da yankin ya samu jiha ta shida.

“Dole ne zababben shugaban kasa ya tabbatar da cewa dukkan kofofin tattalin arziki a fadin kasar nan da suka hada da sake bude mashigar ruwa ta Kalaba, yaye kogin Azumiri, yi wa ‘yan kungiyar IPOB afuwa, da kuma biyan diyya ga iyalan da aka kashe tsawon shekaru.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kabilar IgboNnamdi KanuSharadiTinubuZaman Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Tana Son Ba Da Gudummawar Hikima Don Inganta Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankin Gabas Ta Tsakiya

Next Post

Ministocin Harkokin Wajen Saudiyya Da Iran Sun Gana Da Juna A Karon Farko A Beijing Karkashin Kokarin Sin 

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

16 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

1 day ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

2 days ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

2 days ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

2 days ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Ministocin Harkokin Wajen Saudiyya Da Iran Sun Gana Da Juna A Karon Farko A Beijing Karkashin Kokarin Sin 

Ministocin Harkokin Wajen Saudiyya Da Iran Sun Gana Da Juna A Karon Farko A Beijing Karkashin Kokarin Sin 

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.