• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ohanaeze Ta Bukaci Tinubu Ya Saki Nnamdi Kanu Idan Aka Rantsar Da Shi

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Ohanaeze Ta Bukaci Tinubu Ya Saki Nnamdi Kanu Idan Aka Rantsar Da Shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da Nijeriya ke kara kusantar ranar 29 ga watan Mayu, da za a rantsar da zababben shugaba kasa, kungiyar Ohanaeze Ndigbo, ta fitar da wasu bukatu hudu da ta ke so Bola Tinubu, ya cika domin kwantar da hankalin ‘yan kabilar Igbo.

Babban Sakataren kungiyar Ohanaeze, Okechukwu Isiguzoro, ya ce ya kamata Tinubu ya saki Nnamdi Kanu, shugaban masu fafutukar kafa kasar Biyafra (IPOB), ba tare da wani sharadi ba.

  • Sin: Fannin Sayayya Da Na Yawon Shakatawa Na Kara Farfadowa A Rubu’in Farko Na Bana
  • Gwamnatin Kaduna Ta Sassauta Dokar Zirga-Zirga Da Ta Saka A Wasu Yankuna

Isiguzoro, ya ce sakin Kanu zai dawo da zaman lafiya da tsaro a yankin Kudu maso Gabashin kasar nan.

Ya yi nuni da cewa, dole ne Tinubu ya tabbatar da yankin Kudu maso Gabas ya samar da shugaban majalisar dattawa.

Jigon na Ohanaeze, ya ce dole ne Tinubu ya tabbatar da ganin an kirkiri jiha ta shida a yankin kudu maso Gabas.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

A cewar Isiguzoro: “Tinubu mai son ci gaba ne, shi mai dabara ne; gwamnatin Tinubu ba za ta zama kamar gwamnatin Buhari ba.

“Matsalar Tinubu, ita ce yawan shekaru, da kuma mafi yawan mutanen da suka sa Buhari bai yi nasara ba suna bayansa saboda wasu kalubalen da ya ke fuskanta biyo bayan zaben 2023.

“Dole ne Tinubu ya tabbatar wa da yankin Kudu maso Gabas wadannan muhimman bukatu hudu don yankin ya amince da shi a matsayin shugaban Nijeriya, kana kabilar Igbo su tsaya tsayin-daka su kare mulkinsa.

“Na farko shi ne, dole ne Tinubu ya maido da zaman lafiya da tsaro ba tare da wani sharadi ba ta hanyar sakin Nnamdi Kanu, ko zai ba shi afuwar shugaban kasa a lokacin jawabin karbar mulkinsa ko kuma ya yi amfani da karfin ikon shugaban kasa wajen ganin an sake shi domin dawo da zaman lafiya da tsaro a yankin kudu maso gabas.

“Na biyu, dole ne Tinubu ya fara aikin warkarwa wurin ganin ya daidaita tikitin Musulmi da Musulmi a takarar shugaban kasa ta hanyar bai wa Kirista daga Kudu maso Gabas shugaban majalisar dattawa. Duk wanda zai zama Shugaban Majalisar Dattawa ka da ya zama wani Sanata mai mukami a majalisar wadanda ba shi da kishin kasa.

“Muna kira ga majalisar dattawa da ta gyara dokokinta tare da ba da izinin sababbin ‘yan majalisa su jagorancin majalisar saboda Sanatocin da ke rike da mukamin akwai shakku a kan su kuma ba za su iya kare muradun Ndigbos (kabilar Igbo) ba.

“Na uku, dole ne Tinubu ya sanya tsarin siyasa da zai tabbatar da cewa ‘yan kabilar Igbo sun ga alkawarin da Buhari ya yi masu a asirce cewa zai tabbatar da yankin ya samu jiha ta shida.

“Dole ne zababben shugaban kasa ya tabbatar da cewa dukkan kofofin tattalin arziki a fadin kasar nan da suka hada da sake bude mashigar ruwa ta Kalaba, yaye kogin Azumiri, yi wa ‘yan kungiyar IPOB afuwa, da kuma biyan diyya ga iyalan da aka kashe tsawon shekaru.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kabilar IgboNnamdi KanuSharadiTinubuZaman Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Tana Son Ba Da Gudummawar Hikima Don Inganta Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankin Gabas Ta Tsakiya

Next Post

Ministocin Harkokin Wajen Saudiyya Da Iran Sun Gana Da Juna A Karon Farko A Beijing Karkashin Kokarin Sin 

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

6 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

8 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

1 day ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

1 day ago
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

2 days ago
Next Post
Ministocin Harkokin Wajen Saudiyya Da Iran Sun Gana Da Juna A Karon Farko A Beijing Karkashin Kokarin Sin 

Ministocin Harkokin Wajen Saudiyya Da Iran Sun Gana Da Juna A Karon Farko A Beijing Karkashin Kokarin Sin 

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.