• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Oluremi Tinubu Ta Tallafa Wa Tsofaffi 250 Da N100,000 Kowannensu A Kebbi

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
Oluremi Tinubu Ta Tallafa Wa Tsofaffi 250 Da N100,000 Kowannensu A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan Shugaban Kasar Nijeriya, Sanata Oluremi Tinubu, ta raba Naira miliyan 25 ga mabukata 250 ta hanyar shirin Renewed Hope Initiative Elderly Support Scheme (RHIESS) a Jihar Kebbi.

Sanata Oluremi Tinubu ta samu wakilcin uwargidan gwamnan Kebbi, Hajiya Zainab Idris, wadda ita ce ko’odinetan shirin na jihar a babban bugu na RHIESS a Birnin Kebbi.

  • Tinubu Ya Sake Bullo Da Shirin Ciyar Da Dalibai A Makarantu
  • Kotun Ƙoli Ta Kammala Sauraron Ƙarar Zaɓen Kano, Za Ta Sanar Da Ranar Yanke Hukunci

Ta ce, “Wannan shirin ne na tallafa wa marasa galihu 250 ‘yan kasa da suke da shekaru 65 zuwa sama a fadin dukkan jahohin tarayya 36 hadi da babban birnin tarayya da kuma tsofaffi daga kungiyar matan jami’an tsaro na ‘yansanda (DEPOWA).

“Wadannan zababbun wadanda za su ci gajiyar shirin za su karbi kudi Naira 100,000 kowannensu, domin a rage musu radadin talaucin tabarbarewar tattalin arziki da kuma rage wa manyanmu da suke fama da bukata a rayuwasu.”

Matar Shugaban kasa, ta kara da cewa jimillar kudaden da aka fitar sun kai Naira miliyan 950 kamar yadda hukumar gudanarwar kungiyar Renewed Hope Initiative ta amince.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

A cewarta, kowace jiha ta tarayya za ta karbi kudi har Naira miliyan 25 don tallafa wa mutanen jiharsu.

“Mun himmatu wajen ganin kowace jiha ta samu wannan tallafi, ba tare da nuna wariyaba,” in ji ta.

Misis Oluremi Tinubu, wadda ta jaddada muhimmancin ba da fifiko ga tsofaffi a cikin shirin, ta ce kula da su wani bangare ne na girmama su da gudunmawar da suka bayar tare da amincewa da haduwar da suka fuskanta.

Haka zalika ta ce “Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu za ta ba da kulawa ga manyan ‘yan kasarmu, haka kuma za a ba da fifiko ga kiwon lafiyarku, ilimin yara kananan, don rage muku walhalhalu rayuwa.

A wani bangare na tallafin da jihar ke bai wa shirin, sakatariyar dindindin ta ma’aikatar harkokin mata da ci gaban jama’a ta jihar, Hajiya Aisha Maikurata, ta bayyana cewa gwamnatin jihar ta kaddamar da tallafin ba da kiwon lafiya a kyauta tare da raba kayan abinci iri-iri ga dattawan jihar.

“Ma’aikatarmu tana tallafa wa tsofaffi, gajiyayyu da masara galihu da kuma masu karamin karfi a kyauta tare da rarraba sauran kayayyaki ga wadanda suka amfana kamar yadda ya kamata, don tabbatar da nasarar wannan shirin,” in ji ta.

Hajiya Aisha Maikurata ta gode wa uwargidan shugaban kasa da gwamnatin jihar da kuma uwargidan gwamnan bisa kokarinsu na ganin an samu nasarar raba wa wadanda suka ci gajiyar tallafin.

Da yake mika godiyarsa ga uwargidan shugaban kasar, Alhaji Ahmad Mahmud, wanda ya yi magana a madadin wadanda suka ci gajiyar tallafin, ya bayar da tabbacin cewa za a yi amfani da wannan karimcin cikin adalci domin cimma burin da aka sa a gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Bikin Nuna Fim Mai Taken “Peking Man, The Last Secret of Humankind” Karo Na Farko A Hedkwatar UNESCO

Next Post

Sin Za Ta Daidaita Haraji Kan Hajojin Da Ake Shige Da Ficen Su A 2024

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2 hours ago
Tinubu
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

2 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

3 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

6 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

9 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

10 hours ago
Next Post
Sin Za Ta Daidaita Haraji Kan Hajojin Da Ake Shige Da Ficen Su A 2024

Sin Za Ta Daidaita Haraji Kan Hajojin Da Ake Shige Da Ficen Su A 2024

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Tinubu

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.