• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Oluremi Tinubu Ta Tallafa Wa Tsofaffi 250 Da N100,000 Kowannensu A Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Oluremi Tinubu Ta Tallafa Wa Tsofaffi 250 Da N100,000 Kowannensu A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan Shugaban Kasar Nijeriya, Sanata Oluremi Tinubu, ta raba Naira miliyan 25 ga mabukata 250 ta hanyar shirin Renewed Hope Initiative Elderly Support Scheme (RHIESS) a Jihar Kebbi.

Sanata Oluremi Tinubu ta samu wakilcin uwargidan gwamnan Kebbi, Hajiya Zainab Idris, wadda ita ce ko’odinetan shirin na jihar a babban bugu na RHIESS a Birnin Kebbi.

  • Tinubu Ya Sake Bullo Da Shirin Ciyar Da Dalibai A Makarantu
  • Kotun Ƙoli Ta Kammala Sauraron Ƙarar Zaɓen Kano, Za Ta Sanar Da Ranar Yanke Hukunci

Ta ce, “Wannan shirin ne na tallafa wa marasa galihu 250 ‘yan kasa da suke da shekaru 65 zuwa sama a fadin dukkan jahohin tarayya 36 hadi da babban birnin tarayya da kuma tsofaffi daga kungiyar matan jami’an tsaro na ‘yansanda (DEPOWA).

“Wadannan zababbun wadanda za su ci gajiyar shirin za su karbi kudi Naira 100,000 kowannensu, domin a rage musu radadin talaucin tabarbarewar tattalin arziki da kuma rage wa manyanmu da suke fama da bukata a rayuwasu.”

Matar Shugaban kasa, ta kara da cewa jimillar kudaden da aka fitar sun kai Naira miliyan 950 kamar yadda hukumar gudanarwar kungiyar Renewed Hope Initiative ta amince.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

A cewarta, kowace jiha ta tarayya za ta karbi kudi har Naira miliyan 25 don tallafa wa mutanen jiharsu.

“Mun himmatu wajen ganin kowace jiha ta samu wannan tallafi, ba tare da nuna wariyaba,” in ji ta.

Misis Oluremi Tinubu, wadda ta jaddada muhimmancin ba da fifiko ga tsofaffi a cikin shirin, ta ce kula da su wani bangare ne na girmama su da gudunmawar da suka bayar tare da amincewa da haduwar da suka fuskanta.

Haka zalika ta ce “Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu za ta ba da kulawa ga manyan ‘yan kasarmu, haka kuma za a ba da fifiko ga kiwon lafiyarku, ilimin yara kananan, don rage muku walhalhalu rayuwa.

A wani bangare na tallafin da jihar ke bai wa shirin, sakatariyar dindindin ta ma’aikatar harkokin mata da ci gaban jama’a ta jihar, Hajiya Aisha Maikurata, ta bayyana cewa gwamnatin jihar ta kaddamar da tallafin ba da kiwon lafiya a kyauta tare da raba kayan abinci iri-iri ga dattawan jihar.

“Ma’aikatarmu tana tallafa wa tsofaffi, gajiyayyu da masara galihu da kuma masu karamin karfi a kyauta tare da rarraba sauran kayayyaki ga wadanda suka amfana kamar yadda ya kamata, don tabbatar da nasarar wannan shirin,” in ji ta.

Hajiya Aisha Maikurata ta gode wa uwargidan shugaban kasa da gwamnatin jihar da kuma uwargidan gwamnan bisa kokarinsu na ganin an samu nasarar raba wa wadanda suka ci gajiyar tallafin.

Da yake mika godiyarsa ga uwargidan shugaban kasar, Alhaji Ahmad Mahmud, wanda ya yi magana a madadin wadanda suka ci gajiyar tallafin, ya bayar da tabbacin cewa za a yi amfani da wannan karimcin cikin adalci domin cimma burin da aka sa a gaba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Bikin Nuna Fim Mai Taken “Peking Man, The Last Secret of Humankind” Karo Na Farko A Hedkwatar UNESCO

Next Post

Sin Za Ta Daidaita Haraji Kan Hajojin Da Ake Shige Da Ficen Su A 2024

Related

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara
Tsaro

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

1 hour ago
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa
Labarai

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

2 hours ago
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya
Labarai

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

3 hours ago
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC
Labarai

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

4 hours ago
Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya
Labarai

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

7 hours ago
Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa
Labarai

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

8 hours ago
Next Post
Sin Za Ta Daidaita Haraji Kan Hajojin Da Ake Shige Da Ficen Su A 2024

Sin Za Ta Daidaita Haraji Kan Hajojin Da Ake Shige Da Ficen Su A 2024

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.