ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Oluremi Tinubu Ta Tallafa Wa Tsofaffi 250 Da N100,000 Kowannensu A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
Tinubu

Uwargidan Shugaban Kasar Nijeriya, Sanata Oluremi Tinubu, ta raba Naira miliyan 25 ga mabukata 250 ta hanyar shirin Renewed Hope Initiative Elderly Support Scheme (RHIESS) a Jihar Kebbi.

Sanata Oluremi Tinubu ta samu wakilcin uwargidan gwamnan Kebbi, Hajiya Zainab Idris, wadda ita ce ko’odinetan shirin na jihar a babban bugu na RHIESS a Birnin Kebbi.

  • Tinubu Ya Sake Bullo Da Shirin Ciyar Da Dalibai A Makarantu
  • Kotun Ƙoli Ta Kammala Sauraron Ƙarar Zaɓen Kano, Za Ta Sanar Da Ranar Yanke Hukunci

Ta ce, “Wannan shirin ne na tallafa wa marasa galihu 250 ‘yan kasa da suke da shekaru 65 zuwa sama a fadin dukkan jahohin tarayya 36 hadi da babban birnin tarayya da kuma tsofaffi daga kungiyar matan jami’an tsaro na ‘yansanda (DEPOWA).

ADVERTISEMENT

“Wadannan zababbun wadanda za su ci gajiyar shirin za su karbi kudi Naira 100,000 kowannensu, domin a rage musu radadin talaucin tabarbarewar tattalin arziki da kuma rage wa manyanmu da suke fama da bukata a rayuwasu.”

Matar Shugaban kasa, ta kara da cewa jimillar kudaden da aka fitar sun kai Naira miliyan 950 kamar yadda hukumar gudanarwar kungiyar Renewed Hope Initiative ta amince.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

A cewarta, kowace jiha ta tarayya za ta karbi kudi har Naira miliyan 25 don tallafa wa mutanen jiharsu.

“Mun himmatu wajen ganin kowace jiha ta samu wannan tallafi, ba tare da nuna wariyaba,” in ji ta.

Misis Oluremi Tinubu, wadda ta jaddada muhimmancin ba da fifiko ga tsofaffi a cikin shirin, ta ce kula da su wani bangare ne na girmama su da gudunmawar da suka bayar tare da amincewa da haduwar da suka fuskanta.

Haka zalika ta ce “Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu za ta ba da kulawa ga manyan ‘yan kasarmu, haka kuma za a ba da fifiko ga kiwon lafiyarku, ilimin yara kananan, don rage muku walhalhalu rayuwa.

A wani bangare na tallafin da jihar ke bai wa shirin, sakatariyar dindindin ta ma’aikatar harkokin mata da ci gaban jama’a ta jihar, Hajiya Aisha Maikurata, ta bayyana cewa gwamnatin jihar ta kaddamar da tallafin ba da kiwon lafiya a kyauta tare da raba kayan abinci iri-iri ga dattawan jihar.

“Ma’aikatarmu tana tallafa wa tsofaffi, gajiyayyu da masara galihu da kuma masu karamin karfi a kyauta tare da rarraba sauran kayayyaki ga wadanda suka amfana kamar yadda ya kamata, don tabbatar da nasarar wannan shirin,” in ji ta.

Hajiya Aisha Maikurata ta gode wa uwargidan shugaban kasa da gwamnatin jihar da kuma uwargidan gwamnan bisa kokarinsu na ganin an samu nasarar raba wa wadanda suka ci gajiyar tallafin.

Da yake mika godiyarsa ga uwargidan shugaban kasar, Alhaji Ahmad Mahmud, wanda ya yi magana a madadin wadanda suka ci gajiyar tallafin, ya bayar da tabbacin cewa za a yi amfani da wannan karimcin cikin adalci domin cimma burin da aka sa a gaba.

Tinubu
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Nijeriya Da Jamhuriyar Benin Za Su Sassauta Tsanantawa A Kan Iyakokinsu Ga ‘Yan Kasuwa
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Hajjin Bana: Shettima Zai Kaddamar Da Jirgin Farko Na Maniyyata 430 A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Jami’an Tsaro sun Ceto Mata Biyu da aka Yi Garkuwa da Su A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk-2/
    Majalisar Dokokin Kebbi Ta Dakatar Da Dan Majalisa Mai Wakiltar Birnin Kebbi Ta Arewa

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano
Labarai

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
Next Post
Sin Za Ta Daidaita Haraji Kan Hajojin Da Ake Shige Da Ficen Su A 2024

Sin Za Ta Daidaita Haraji Kan Hajojin Da Ake Shige Da Ficen Su A 2024

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.