• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP: Gwamnan Bala Ya Kalubalanci Wike Kan Kunno Wutar Rikicin Jam’iyya A Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
PDP: Gwamnan Bala Ya Kalubalanci Wike Kan Kunno Wutar Rikicin Jam’iyya A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban ƙungiyar gwamnonin PDP kuma gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad, ya ce, babu wata jam’iyyar siyasa da ba ta fuskantar ‘yan rikice-rikice ko da kuwa ta na da cikakken tsarin shugabanci.

 

Kazalika, gwamnan ya kuma maida martani kan iƙirarin baya-bayan nan da ministan birnin tarayya, Nyesom Wike, ya yi da ke cewa zai kunna wuta ga wasu gwamnonin jihohi na PDP kan yunƙurin kwace tsarin jam’iyyar a jihar Ribas, Bala ya ce, babu wanda ya isa ya kunno wuta a jihar Bauchi domin akwai wadatacccen ruwa da zai iya faca-faca da wutar.

  • An Masa Daurin Watanni 4 Kan Satar iPhone Guda 2
  • Ambaliya: Aminu Dantata Ya Bai Wa Maiduguri Tallafin Naira Biliyan 1.5

Gwamnan wanda ke wannan maganar a ranar Talata 17 ga watan Satumba, yayin da ya karɓi bakwancin shugabanni jam’iyyar PDP na ƙasa da suka kawo masa ziyarar mara baya a jihar Bauchi, ya yi tilawar cewa, mafi yawan ayyukan raya ƙasar nan jam’iyyar PDP ce ta yi su.

 

Labarai Masu Nasaba

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Ya ce: “Ba wata jam’iyya da ta tsira ga kananan rikici na sabani, don haka, ya sa aka samu jagoranci saboda daidaita sabani da ajiye komai a inda ya dace.

 

“Dole ne mu yi abubuwa bisa doka da oda na jam’iyya, dole mu mutunta mutane, dole mu jingine ra’ayinmu a gefe, dole mu mutunta banbance-banbancenmu, kuma dole su ajiye matsayin jam’iyyar a saman kowa da mutunta jimammen tarihin jam’iyyar.”

 

Bala Muhammad ya kuma ce, jagoranci jam’iyyar a ɗinke yake kuma babu mai shigo da ra’ayin ƙashin kansa cikin lamuran.

 

Ya misalta cewa abota daban, mulki daban, kuma lamuran da suka shafi jam’iyya daban, don haka ya yi hannunka mai sanda ga abokin nasa Wike da cewa ba za su bari wani abu ya addabi jam’iyyar ba.

 

Ya kuma sanar da cewa, za su tattauna muhimman abubuwan da suka shafi ci gaban jam’iyyar PDP.

 

Tun da farko a jawabinsa, jagoran tawagar, kuma mai bai wa jam’iyyar shawara kan harkokin Shari’a, Kamaldeen Adeyemi Ajibade SAN, ya ce PDP na alfahari da yadda ta ga gwamnan na gudanar da wakilci na kwarai ta hanyar shimfiɗa nagartattun ayyuka da ya zaman musu abun alfahari a jihar.

 

Ya ce sun kuma zo ne domin nuna goyon baya domin ƙara wa gwamnan karfin gwiwa kan himma da azamarsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Kasar Sin Ya Bukaci Amurka Da Ta Matsawa Isra’ila Ta Dakatar Da Ayyukan Soji A Gaza

Next Post

An Kammala Bikin Baje Kolin CIFTIS Tare Da Nasarori Masu Tarin Yawa

Related

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya
Labarai

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

10 hours ago
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

12 hours ago
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista
Labarai

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

14 hours ago
Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi

16 hours ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

18 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

18 hours ago
Next Post
An Kammala Bikin Baje Kolin CIFTIS Tare Da Nasarori Masu Tarin Yawa

An Kammala Bikin Baje Kolin CIFTIS Tare Da Nasarori Masu Tarin Yawa

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.