• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Fitar Da Jaddawalin Babban Taronta Na Shiyyoyi Na 2025

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
PDP

Kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyar PDP ya amince da jadawalin taron shiyoyi na 2025.

Rahotanni sun bayyana cewa za a zabi sabbin mambobin kwamitocin gudanarwa na shiyoyi da kuma shugabannin na shiyoyi a wannan babban taro.

  • Janar Gowon: Tsohon Shugaban Kasa Mafi Tsawon Rai A Nijeriya Na Cika Shekara 90
  • Babu Hannun Mijina A Wahalar Da Ƴan Nijeriya Ke Sha

A wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Abuja, mai magana da yawun jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba, ya ce kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na kasa ya amince da gudanar da taron shiyoyin.

Ya bayyana cewa kwamitin gudanarwa na jam’iyyar ya amince da jadawalin a yayin taronta na 592, gabanin karewar wa’adin shugabannin shiyoyin na Kudu maso Kudu, Kudu maso Gabas, Kudu maso Yamma, Arewa ta Tsakiya da Arewa-maso Gabas.

Sanarwar ta bayyana jadawalin ayyuka, ta ce, “Sayar da fom ga dukkan mukaman na sabbi da tsofaffin shugabannin shiyoyi na kasa a Kudu maso Kudu, Kudu maso Gabas, Kudu maso Yamma, Arewa ta Tsakiya da Arewa maso Gabas: Litinin, 18 ga Nuwamban 2024 zuwa ranar Laraba, 18 ga Disamban 2024.

LABARAI MASU NASABA

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

“Wa’adin karshe na miyar da fom din takara zai kasance a ranar Juma’a, 17 ga Janairun 2025.

“Tantance ‘yan takara a hedikwatar shiyya, zai kasance ranar Asabar, 25 ga Janairu, 2025.

“Amincewa da tantance ‘yan takara a hedkwatar shiyya, zai kasance ranar Asabar, 1 ga Fabrairu, 2025.

“Wallafa sunayen ‘yan takara, zai kasance ranar Laraba, 12 ga Fabrairun 2025. Buga jerin sunayen wakilai, zai kasance ranar Alhamis, 13 ga Fabrairun 2025.

“Ranakun babban taron shiyoyin na Arewa maso Gabas, Kudu maso Gabas, da Kudu maso Kudu, zai kasance ranar Asabar, 22 ga Fabrairun 2025.

“Amincewa da babban taron shiyoyin, zai kasance ranar Talata, 25 ga Fabrairu, 2025.

“Babban taron shiyoyi na shiyyar Arewa ta Tsakiya da Kudu maso Yamma, zai gudana a ranar Asabar, 22 ga Maris, 2025. Amincewa da babban taron, zai kasance ranar Laraba, 26 ga Maris, 2025.”

Jam’iyyar ta bukaci duk masu son yin takara da su tuntubi sakatariyar jam’iyyar na kasa don samun bayanai kan kudaden da ake bukata da sauran tambayoyi.

Ologunagba ya kuma ja hankalin dukkan shugabannin PDP da masu ruwa da tsaki, da ’ya’yan jam’iyyar da su ci gaba da hada kan su, su kuma yi kokarin ganin jam’iyyar ta samu ci gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya
Tambarin Dimokuradiyya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Next Post
Nijeriya Ta Doke Kasar Libya A Akwa Ibom

Nijeriya Ta Doke Kasar Libya A Akwa Ibom

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

October 14, 2025
Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

October 14, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

October 14, 2025
Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.