ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Fitar Da Jaddawalin Babban Taronta Na Shiyyoyi Na 2025

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Kwamitin gudanarwa na kasa na jam’iyyar PDP ya amince da jadawalin taron shiyoyi na 2025.

Rahotanni sun bayyana cewa za a zabi sabbin mambobin kwamitocin gudanarwa na shiyoyi da kuma shugabannin na shiyoyi a wannan babban taro.

  • Janar Gowon: Tsohon Shugaban Kasa Mafi Tsawon Rai A Nijeriya Na Cika Shekara 90
  • Babu Hannun Mijina A Wahalar Da Ƴan Nijeriya Ke Sha

A wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin a Abuja, mai magana da yawun jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba, ya ce kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na kasa ya amince da gudanar da taron shiyoyin.

ADVERTISEMENT

Ya bayyana cewa kwamitin gudanarwa na jam’iyyar ya amince da jadawalin a yayin taronta na 592, gabanin karewar wa’adin shugabannin shiyoyin na Kudu maso Kudu, Kudu maso Gabas, Kudu maso Yamma, Arewa ta Tsakiya da Arewa-maso Gabas.

Sanarwar ta bayyana jadawalin ayyuka, ta ce, “Sayar da fom ga dukkan mukaman na sabbi da tsofaffin shugabannin shiyoyi na kasa a Kudu maso Kudu, Kudu maso Gabas, Kudu maso Yamma, Arewa ta Tsakiya da Arewa maso Gabas: Litinin, 18 ga Nuwamban 2024 zuwa ranar Laraba, 18 ga Disamban 2024.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

“Wa’adin karshe na miyar da fom din takara zai kasance a ranar Juma’a, 17 ga Janairun 2025.

“Tantance ‘yan takara a hedikwatar shiyya, zai kasance ranar Asabar, 25 ga Janairu, 2025.

“Amincewa da tantance ‘yan takara a hedkwatar shiyya, zai kasance ranar Asabar, 1 ga Fabrairu, 2025.

“Wallafa sunayen ‘yan takara, zai kasance ranar Laraba, 12 ga Fabrairun 2025. Buga jerin sunayen wakilai, zai kasance ranar Alhamis, 13 ga Fabrairun 2025.

“Ranakun babban taron shiyoyin na Arewa maso Gabas, Kudu maso Gabas, da Kudu maso Kudu, zai kasance ranar Asabar, 22 ga Fabrairun 2025.

“Amincewa da babban taron shiyoyin, zai kasance ranar Talata, 25 ga Fabrairu, 2025.

“Babban taron shiyoyi na shiyyar Arewa ta Tsakiya da Kudu maso Yamma, zai gudana a ranar Asabar, 22 ga Maris, 2025. Amincewa da babban taron, zai kasance ranar Laraba, 26 ga Maris, 2025.”

Jam’iyyar ta bukaci duk masu son yin takara da su tuntubi sakatariyar jam’iyyar na kasa don samun bayanai kan kudaden da ake bukata da sauran tambayoyi.

Ologunagba ya kuma ja hankalin dukkan shugabannin PDP da masu ruwa da tsaki, da ’ya’yan jam’iyyar da su ci gaba da hada kan su, su kuma yi kokarin ganin jam’iyyar ta samu ci gaba.

PDP
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

PDP
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Nijeriya Ta Doke Kasar Libya A Akwa Ibom

Nijeriya Ta Doke Kasar Libya A Akwa Ibom

LABARAI MASU NASABA

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

June 5, 2026
An Cafke Motocin Dako 50 Makare Da Abinci Za Su Shiga Nijar A Zamfara

Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal

June 5, 2026
Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi

June 5, 2026
An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe

June 5, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Ma’aurata A Abuja

June 5, 2026
Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi

June 5, 2026
An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

An Yi Suka Kan Mayar Da Nijeriya Jujin Jibge Kwantaina Da Ake Shigowa Da Su

June 5, 2026
Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

June 5, 2026
Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Sabon Rikicin Manoma Da Makiyaya yayi Ajalin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 5, 2026
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.