Rundunar ‘yantar da jama’ar kasar Sin (PLA) a sashen kudancin kasar ta gudanar da atisayen hadin gwiwa na sojan ruwa da na sararin sama a tekun kudancin kasar Sin daga ranar 7 zuwa 8 ga watan Afrilu, a cewar babban kanal Tian Junli, mai magana da yawun rundunar ta PLA a sashen kudancin kasar, a cikin wata sanarwa a yau Talata.
Dakarun rundunar a sashen kudancin kasar sun kasance cikin shirin ko-ta-kwana a kowane lokaci, don tabbatar da ikon mulkin kasar Sin da tsaron kasar da kuma hakki da muradun teku na kasar Sin, a cewar Tian. (Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp