Ƙungiyar kwallon kafa ta PSG na neman daukar dan wasan Barcelona, Lamine Yamal a kan kudi Yuro Miliyan 200.
PSG na neman wanda zai maye mata gurbin dan wasanta, Klylian Mbappe idan ya bar kungiyar inda ake alakanta shi da komawa Real Madrid, a karshen kakar wasa ta bana.
- EFCC Ta Sake Maka Emefiele A Kotu Kan Wasu Sabbin Tuhume-tuhume 4
- Unai Emery Ya Sabunta Kwantaraginsa A Aston Villa
Goal ta bayyana cewar akwai kyakkyawar alaka tsakanin daraktan wasanni na PSG, Luis Campos da wakilin Yamine Yamal, Jorge Mendes wanda ake hasashen hakan zai iya saukaka wa Le Perisien wajen daukar matashin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp