Gwamnatin tarayya ta baiwa ko wacce jiha Naira biliyan biyu ciki har da Abuja daga cikin Naira biliyan biyar na tallafi da gwamnatin ta sanar a kwanan baya za ta baiwa Gwamnoni domin rage radadin cire tallafin mai.
Ministan kudi da tattalin arzikin kasa, Wale Edun ne ya shaida wa manema labarai hakan a Abuja.
Edun ya ce, wadannan kudaden, ba sa daga cikin kudin da gwamnatin ke son karbo wa rance na dala miliyan 800 daga Bankin duniya domin rage radadin cire tallafin man.
A cewarsa, gwamnatin ba ta son fitar da kudaden tallafin a lokaci daya, inda hakan ya sa ta dakatar da tura sauran Naira biliyan Ukun don kauce wa kara hauhawar farashin kayan masarufi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp