• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Atiku Ga Tinubu: Fada Wa ‘Yan Nijeriya Yadda Ka Samu Digiri Ba Tare Da Firamare Da Sakandare Ba

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Atiku Ga Tinubu: Fada Wa ‘Yan Nijeriya Yadda Ka Samu Digiri Ba Tare Da Firamare Da Sakandare Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, ya sake caccaki takardun makarantar Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu.

Atiku ya kalubalanci sahihancin takardar shaidar digirin Tinubu da jami’ar Chicago ta Amurka ta bayar, ya ce karatun shugaban kasar na ci gaba da zama babbar abun tantama.

  • Sakaci: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Shugaban Asibitin Hasiya Bayero
  • Tottenham Da Chelsea Na Zawarcin Ansu Fati Na Barcelona

A wani sako da ya wallafa ta shafinsa na Tuwita, Atiku ya zargi shugaban kasar da kaurace kawo takardun karatunsa na firamare da sakandare amma sai ya kawo na digiri daga jami’ar Chicago.

A cewar tsohon mataimakin shugaban kasar, a shekarar 1999, Tinubu ya yi ikirarin cewa ya halarci makarantar firamare ta St. John’s da ke Aroloya a Legas, kafin ya wuce makarantar ‘Children’s Home’ da ke Ibadan.

Ya yi zargin cewa shaidar karatun Shugaba Tinubu a 2023 ya sha bamban da wanda aka gabatar a shekarar 1999, inda ya kara da cewa shugaban kasar ya ce ya halarci jami’ar Chicago ba tare da karatun firamare da sakandare ba.

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

“Na farka da safiyar yau ina mamakin yadda muka sami wannan lamari. A cikin 1999, Tinubu ya yi ikirarin cewa ya halarci makarantar firamare ta St. John da ke Aroloya a Legas, kafin ya wuce zuwa makarantar ‘Children Home’ a Ibadan.”

“A cewarsa, ci gaba da karatu kwalejin gwamnati ta Ibadan da kwalejin Richard Daley da jami’ar Chicago ta Amurka.

“Abin mamakin shi ne, a 2023, Tinubu ya ce shi dai kwai ya halarci jami’ar Chicago kadai. Ina ta mamakin ko ta yaya hakan zai yiwu? Yana tunanin cewa ’yan Nijeriya ba za su shiga rudani ba kamar yadda na shiga cewa, Tinubu ba shi da takardar firamare da sakandare amma ya yi digiri a jami’a. Kuna iya tambayar Tinubu yadda ya samu wannan nasarar domin mu yi koyi da hazakarsa,” Atiku ya rubuta.

A watan Maris ne aka ayyana Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa na 2023. Amma Atiku ya ci gaba da kalubalantar sakamakon zaben a kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa, inda ya kalubalanci sahihancin takardun makarantar shugaban kasa.

Ya kuma garzaya wata kotun Amurka da ke gundumar Arewacin Jihar Illinois a Chicago, domin neman tilastawa jami’ar Chicago sakin bayanan karatun Tinubu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abinda Ya Kamata A Sani Game Da Jadawalin Gasar Kofin Zakarun Turai Na Bana 

Next Post

Goyon Bayan Da Amurka Ta Baiwa Japan Game Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Ba Shi Da Amfani

Related

Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

23 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

24 hours ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

1 day ago
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

3 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

3 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

4 weeks ago
Next Post
Japan

Goyon Bayan Da Amurka Ta Baiwa Japan Game Da Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Ba Shi Da Amfani

LABARAI MASU NASABA

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.