• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

by Khalid Idris Doya
3 weeks ago
in Labarai
0
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da raguwar hauhawar farashin kayayyaki da aka samu karo na hudu a jere a Nijeriya, ‘yan kasar da ‘yan kasuwa ba su samu saukin da ake tsammani yadda ya kamata ba.

Rahotanni sun nuna cewa hauhawar farashi ya ragu zuwa kaso 21.88 a cikin 100 a watan Yuli daga kaso 22.22 a watan Yuni.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Tawagar Shugaban kasa Bola Tinubu sun nuna farin cikinsu da raguwar tare da misalta hakan bisa kyakkyawar tsarin shugabanci da kasar ke samu tsawon shekaru biyu da suka gabata.

Wannan kuma na zuwa ne a yayin da tattalin arzikin kasar ya karu zuwa naira tiriliyan 372.8 a shekarar 2024 kuma ya sake samun tagomashi a watan Yulin 2025.

Kila wannan dalilin ne ya sanya tsohon ministan kudi, Ngozi Okonjo-Iweala, ta ce, tattalin arzikin Nijeriya na daidaituwa, a lokacin da ta ziyarci Shugaban kasa Tinubu a kwanakin baya.

Labarai Masu Nasaba

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Duk da wannan matakin, ‘yan Nijeriya da ‘yan kasuwa na ci gaba da nuna damuwa kan cewa ba su ga alamar raguwar hauhawar a zahirance cikin tattalin arziki ba.

Farashin kayayyakin bukata daga na abinci zuwa na mai ba su yi sauka sosai yadda jama’a suke fata ko suke tsammani ba, hakazalika, kudin wuta, da tsadar kudaden sufuri duk suna nan ba sauki, sannan farashin makamashi dukka haka nan.

Da yake tofa albarkacin bakinsu, tsohon shugaban cibiyar hada-hadar banki a Nijeriya (CIBN), Mazi Okechukwu Unegbu da babban jami’in gudanarwar SD & D Capital Management, Gbolade Idakolo da fitaccen masanin tattalin arzikin nan, Farfesa Segun Ajibola, sun bayyana ra’ayoyinsu kan raguwar hauhawar farashin kayayyakin masarufi a watan Yuli.

A bangarensa, babban jami’in gudanarwar SD & D Capital Management, Gbolade Idakolo, ya bayyana cewar hauhawar farashin kayan abinci a Nijeriya na ci gaba da karuwa sakamakon matsalolin tsaro da kuma kalubalen farashin canjin kudade a yankunan da ake fitar da amfanin gona.

“Ainihin hauhawar farashin kayayyaki ya ragu a karo na hudu a jere ne saboda matsayin Babban Bankin Nijeriya kan MPR da sauran ayyukan da suka shafi tattalin arziki.

“Duk da haka, hauhawar farashin kayan abinci na ci gaba da hauhawa saboda rashin tsaro a yankunan noma da kuma kalubalen musayar kayan amfanin gona da ake shigo da su daga kasashen waje.

“Akwai bukatar gwamnatin tarayya ta zage damtse wajen fito da shirye-shiryen da suka dace da zai kai ga rage tsadar kayan abinci a kasar nan,” ya shaida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Farashi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Next Post

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

7 hours ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

8 hours ago
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

10 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

11 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

14 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

15 hours ago
Next Post
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.