• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ramadan: Fasto Ya Raba Wa Musulmi Kayan Masarufi A Kaduna

by Abubakar Abba
2 years ago
in Kananan Labarai
0
Ramadan: Fasto Ya Raba Wa Musulmi Kayan Masarufi A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fitaccen fasto a Jihar Kaduna mai gabatar da wa’azi a Cocin Christ Evangelical and life Intercessory Ministry da ke a anguwar Sabon Tasha Yohanna Buu, ya raba buhun hatsi ga Musulmai mabukata na musaman sama da 1,000 da ke jihar domin su ji dadin yin azumin watan Ramadan na bana.

Buru ya rabar da kayan ne ga masu bukata ta musamman da ke kan titin Kano, inda ya ce, rabar da kayan ya zama wajibi idan aka yi la’akari tsadar kayan masarufi da ke fuskanta a jihar.

  • Hukumar Leken Asiri Ta Amurka Ta Sake Tabka Karya Kan Batun “Nord Stream” 
  • An Yanke Wa Wasu Mutane 4 Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya A Legas

A cewarsa, musulmai masu bukata ta musamman sama da 1000 muke son mu rabarwa da buhunhun masara da gero, inda ya ce, a azumin bara, mun rabar masu da buhunhun amasara, shinkafa da sauran kayan abinci.

Ya ce, a rabon na wannan shekarar, mun hada har da butocin yin sallah da tabarmi, musamman don su yi amfani da su wajen yin sallah da yin addu’oin Allah ya kawo karshen kalubalen rashin tsaro da kasar nan, musamman arewacin kasar ke fuskanta.

Buru ya ce, mahimmancin rabar da kayan shine don a kara karfafa dankon zumunci a tsakanin musulmai da mabiya addinin kiritsa da ke a cikin jihar.

Labarai Masu Nasaba

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

Faston ya kuma yi kira ga masu hannu da shuni da ke jihar da su yi amfani da dukiyoyin su, musamman don ciyar da masu bukata ta musamman da kuma sauran marasa galihu a cikin wannan watan na Ramadan.

Ya kuma yi kira ga ‘yan kasuwa, musamman masu sayar da kayan masarufi da su guji kara farashin don cin kazamar riba a cikin watan na Ramadan.

Daya daga cikin jagororin masu bukata ta musamman da ya karbi kayan a madadin sauran ‘yan uwansa mallan Hassan Lawal Mohammed sarkin kutaren ya mika godiyar su bisa ga tallafin, inda ya ce, yau kimanin shekaru goma kenan Buru na kawo masu irin wannan tallafin.

Bugu da kari wasu makarantun tsangaya da kuma wasu kafafen yada labarai a jihar suma sun amfana da wannan tagomashin na fasto Buru.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FastoKadunaRamadan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Equatorial Guinea

Next Post

CMG Ta Hada Kai Da Manyan Kafafen Yada Labaran Kasashen Afirka Biyar Don Kaddamar Da Wani Shirin TV Mai Suna “More Ci Gaba Tare”

Related

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

2 months ago
Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

3 months ago
Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya
Kananan Labarai

Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya

4 months ago
Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi

5 months ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Kananan Labarai

Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Dala Tiriliyan 7 A Tsarin Kasuwancin Musulunci Na Duniya

10 months ago
Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara
Labarai

Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara

11 months ago
Next Post
CMG Ta Hada Kai Da Manyan Kafafen Yada Labaran Kasashen Afirka Biyar Don Kaddamar Da Wani Shirin TV Mai Suna “More Ci Gaba Tare”

CMG Ta Hada Kai Da Manyan Kafafen Yada Labaran Kasashen Afirka Biyar Don Kaddamar Da Wani Shirin TV Mai Suna “More Ci Gaba Tare”

LABARAI MASU NASABA

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.