• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Yaki Da Talauci Ta Duniya: Sama Da Mutum Biliyan Daya Na Fama Da Talauci – Sakataren MDD

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Ranar Yaki Da Talauci Ta Duniya: Sama Da Mutum Biliyan Daya Na Fama Da Talauci – Sakataren MDD
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban sakataren majalisar dinkin duniya MDD, Antonio Gutteres, acikin jawabinsa na ranar kawar da talauci ta Duniya, ya yi ikirarin cewa, a wannan duniyar ta mu mai cike da dimbin arziki, bai kamata Talauci ya yi ma ta katutu ba.

Gutteres ya ce, duk da dimbin arzikin cikin duniyarmu amma kusan mutane miliyan 700 ke fama da kalubalen rayuwa, inda suke rayuwa a kasa da dala 2.15 daidai da naira N2,000 a duk rana.

  • Ranar Abinci Ta Duniya: Gwamnatin Kaduna Za Ta Samar Da Tsaftataccen Ruwa Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Gwamna Uba Sani Ya Nada Dakta Mayere Sabon Sakataren Gwamnatin Jihar Kaduna

Sama da mutane biliyan daya ne ke fama da matsananciyar rayuwa daga karancin abinci, ruwa, lafiya da ilimi.

Akwai biliyoyin mutanebda ba su da tsaftataccen muhalli, ayyukan yi, wurin kwana ballanta kuma samun ‘yancin zamantakewa.

A halin yanzu, duniyarmu tana fama da rikice-rikicen yaki, rikicin wariya na kara kamari – musamman kan mata da ‘yan mata.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Duk abubuwan da suka janyo koma baya ga ci gaban mu da tsanancin talauci, na da alaka da tsarin tafiyar da harkokin kudi na duniya wanda ya tsufa da kuma rashin adalci wanda ke hana kasashe masu tasowa tallafawa don kawar da talauci da cimma manufar shirin ‘yancin zamantakewa da kawar da talauci na MDD (SDGs).

Kusan mutane miliyan 500 ne za su kasance cikin matsanancin talauci acikin 2030. Wannan, sam ba a abin da za a sa ido ana kallo ba ne kawai, dole a yi wani abu.

A taron koli na SDG da aka yi a watan Satumba, shugabannin kasashen duniya sun amince da bukatar yin garambawul ga tsarin hada-hadar kudi na kasa da kasa, tare da himmatuwa wajen yin wani kwakkwaran shiri don ceto muradun ci gaba mai dorewa da kuma kara kaimi wajen kawar da talauci a ko’ina.

Wannan ya hada da bayar da tallafi don karfafa shirin SDG na akalla dala biliyan 500 a kowace shekara.

Shugabannin sun kuma amince da matakin da aka dauka da niyyar kawar da talauci da wahalhalun rayuwa ga dukkan mutane – daga tsarin samar da abinci da ilimi zuwa ayyukan yi masu nagarta da fadada kariyar zamantakewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Antonio GutteresMDDUN
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar Abinci Ta Duniya: Mata Manoma Zasu Samu Tallafin Aikin Gona A Zamfara

Next Post

Yadda Yaki Da Hamada Ke Samar Da Kudin Shiga A Jihar Xinjiang

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

8 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

10 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

11 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

11 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

13 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

15 hours ago
Next Post
Yadda Yaki Da Hamada Ke Samar Da Kudin Shiga A Jihar Xinjiang

Yadda Yaki Da Hamada Ke Samar Da Kudin Shiga A Jihar Xinjiang

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.