• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Ma’aikata: Bayan Cike Giɓin Albashin Da Muka Gada, Za Mu Ci Gaba Da Inganta Walwalar Ma’aikata – Gwamnan Zamfara

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Ranar Ma’aikata: Bayan Cike Giɓin Albashin Da Muka Gada, Za Mu Ci Gaba Da Inganta Walwalar Ma’aikata – Gwamnan Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani ɓangare na bikin ranar ma’aikata ta bana, Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal ya sake jaddada aniyar gwamnatinsa ta inganta rayuwar ma’aikatan jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne wurin ggagarumin bikin ranar wanda aka saba gudanarwa a duk faɗin ƙasar nan a kowace ranar 1 ga Mayu, wanda na jihar ya gudana a Sakatariyar JB Yakubu da ke Gusau a yau Laraba.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta na nan a kan bakar ta na tafiya tare da ma’aikatan a duk harkokin mulkin jihar.

  • IPMAN Ta Yi Barazanar Rufe Gidajen Mai Sama Da 30,000 Saboda Bashi

 

Sanarwar ta Sulaiman Bala ta ƙara da cewa, a jawabin Gwamnan ga ma’aikata, ya yi alƙawarin aiwatar da tsare-tsaren sa guda shida da ya tsara don haƙƙaƙa shirinsa na tsamo jijar Zamfara daga halin da ya same ta.

Labarai Masu Nasaba

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

“Gwamnatina ta yi na’am da muhimmiyar rawar da ma’aikata ke takawa wajen ƙaddamar da ayyuka da aiwatar da manufofin gwamnati. Ma’aikata da gwamnatoci abokan haɗin gwiwa ne wajen aiwatar da ayyukan ci gaban al’ummarmu.

“Ma’aikata ne ke taimaka wa gwamnati wajen cimma burinta na samar da ayyuka ga jama’a. Bisa la’akari da haka, za mu ci gaba da lalubo hanyoyin inganta jin daɗin ku da na iyalanku, musamman idan aka yi la’akari da irin matsalolin da ake fuskanta a halin yanzu sakamakon cire tallafin man fetur da manufofin kuɗi da ya haifar da koma-baya a darajar Naira da hauhawar farashin kayayyaki da ba a taɓa ganin irinsa ba a ƙasar nan.”

Ma'aikata

Gwamnan ya kuma bayyana wasu nasarorin da gwamnatinsa ta samu a cikin watanni goma sha ɗaya na farko a kan karagar mulki.

“Ya ku ’yan uwana, ina mai farin cikin bayyana cewa a cikin watanni goma sha ɗaya da kafa gwamnatinmu, ma’aikata a Jihar Zamfara suna jin daɗi. Mun fara ta hanyar kawar da giɓin albashin da muka gada tare da tabbatar da biyan albashin akan lokaci, tare da tsawaita wasu abubuwan jin daɗin rayuwar ma’aikata.

“Don ci gaba da wannan yunƙuri, gwamnati ta aiwatar da hanyoyin da za a tabbatar da cewa ma’aikata na gaske ne kaɗai ke cin gajiyar albashinmu. Har ila yau, muna tuntuɓar ma’aikata kan batun albashi, bisa la’akari da yadda rayuwa take a yau. Ina yaba wa da goyon bayan da gwamnatina ke bayarwa da kuma dangantakar da ke tsakaninta da shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago a jihar. Haƙiƙa yana ɗaya daga cikin nasarorin da ake samu na ci gaba wajen maido da inganta harkokin gwamnati.

Bugu da ƙari, Gwamnan na Jihar Zamfara ya yi alƙawarin daidaita dukkan ayyukan gwamnati da kuma gyara ayyukan ma’aikatan gwamnati domin ɗaukar salon gudanar da harkokin gwamnati na zamani.

“Don inganta harkokin gwamnati, nan ba da jimawa ba za mu bayyana tsare-tsaren mu na zamanantar da duk ayyukan gwamnati da kuma sake fasalin ma’aikatan, don aiwatar da tsarin tafiyar da harkokin gwamnati na zamani.

“Wannan zai haɗa da sabbin hanyoyin tantance ayyukan ma’aikata, horarwa da tabbatar da ƙwarewarsu a tsakanin wasu tsare-tsare da dama.

Ma'aikata

“Hakazalika, gwamnati ta ƙuduri aniyar hana zamba da wasu munanan ɗabi’un da suke gurɓata ayyukan gwamnati.

“Saboda sadaukarwar da ma’aikata suka yi a lokacin hidimarsu, ya dace a riƙa girmama su da mutunta su. Wannan ne ya sa muka ɗauki matakin biyan bashin garatuti da gwamnatinmu ta gada. Da zarar mun kawar da basukan, za mu tabbatar da biyan duk waɗanda suka yi ritaya daga ayyukan gwamnati da na ƙananan hukumomi cikin gaggawa.

Ma'aikata

“Da wannan aiki, In Sha Allahu, ma’aikata ba za su sake samun wani dalilin da zai sa su ji shakkar yin ritaya ba, wanda yakan haifar da kwaɗayin ci gaba da aiki.” In ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2024Albashin ma'aikataBikin Ranar Ma'aikataGwamna Dauda LawalZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin Sin Ya Bayar Da Tallafin Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliya Ta Shafa A Kenya

Next Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mutane A Katsina Da Filato

Related

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 
Labarai

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

3 hours ago
Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

6 hours ago
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

8 hours ago
MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama
Manyan Labarai

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

9 hours ago
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

10 hours ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

12 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'adda, Sun Ceto Mutane A Katsina Da Filato

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

September 9, 2025
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

September 9, 2025
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

September 9, 2025
Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

September 9, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

September 9, 2025
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.