• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Ma’aikata: Bayan Cike Giɓin Albashin Da Muka Gada, Za Mu Ci Gaba Da Inganta Walwalar Ma’aikata – Gwamnan Zamfara

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Ranar Ma’aikata: Bayan Cike Giɓin Albashin Da Muka Gada, Za Mu Ci Gaba Da Inganta Walwalar Ma’aikata – Gwamnan Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani ɓangare na bikin ranar ma’aikata ta bana, Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal ya sake jaddada aniyar gwamnatinsa ta inganta rayuwar ma’aikatan jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne wurin ggagarumin bikin ranar wanda aka saba gudanarwa a duk faɗin ƙasar nan a kowace ranar 1 ga Mayu, wanda na jihar ya gudana a Sakatariyar JB Yakubu da ke Gusau a yau Laraba.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu, ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta na nan a kan bakar ta na tafiya tare da ma’aikatan a duk harkokin mulkin jihar.

  • IPMAN Ta Yi Barazanar Rufe Gidajen Mai Sama Da 30,000 Saboda Bashi

 

Sanarwar ta Sulaiman Bala ta ƙara da cewa, a jawabin Gwamnan ga ma’aikata, ya yi alƙawarin aiwatar da tsare-tsaren sa guda shida da ya tsara don haƙƙaƙa shirinsa na tsamo jijar Zamfara daga halin da ya same ta.

Labarai Masu Nasaba

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

“Gwamnatina ta yi na’am da muhimmiyar rawar da ma’aikata ke takawa wajen ƙaddamar da ayyuka da aiwatar da manufofin gwamnati. Ma’aikata da gwamnatoci abokan haɗin gwiwa ne wajen aiwatar da ayyukan ci gaban al’ummarmu.

“Ma’aikata ne ke taimaka wa gwamnati wajen cimma burinta na samar da ayyuka ga jama’a. Bisa la’akari da haka, za mu ci gaba da lalubo hanyoyin inganta jin daɗin ku da na iyalanku, musamman idan aka yi la’akari da irin matsalolin da ake fuskanta a halin yanzu sakamakon cire tallafin man fetur da manufofin kuɗi da ya haifar da koma-baya a darajar Naira da hauhawar farashin kayayyaki da ba a taɓa ganin irinsa ba a ƙasar nan.”

Ma'aikata

Gwamnan ya kuma bayyana wasu nasarorin da gwamnatinsa ta samu a cikin watanni goma sha ɗaya na farko a kan karagar mulki.

“Ya ku ’yan uwana, ina mai farin cikin bayyana cewa a cikin watanni goma sha ɗaya da kafa gwamnatinmu, ma’aikata a Jihar Zamfara suna jin daɗi. Mun fara ta hanyar kawar da giɓin albashin da muka gada tare da tabbatar da biyan albashin akan lokaci, tare da tsawaita wasu abubuwan jin daɗin rayuwar ma’aikata.

“Don ci gaba da wannan yunƙuri, gwamnati ta aiwatar da hanyoyin da za a tabbatar da cewa ma’aikata na gaske ne kaɗai ke cin gajiyar albashinmu. Har ila yau, muna tuntuɓar ma’aikata kan batun albashi, bisa la’akari da yadda rayuwa take a yau. Ina yaba wa da goyon bayan da gwamnatina ke bayarwa da kuma dangantakar da ke tsakaninta da shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago a jihar. Haƙiƙa yana ɗaya daga cikin nasarorin da ake samu na ci gaba wajen maido da inganta harkokin gwamnati.

Bugu da ƙari, Gwamnan na Jihar Zamfara ya yi alƙawarin daidaita dukkan ayyukan gwamnati da kuma gyara ayyukan ma’aikatan gwamnati domin ɗaukar salon gudanar da harkokin gwamnati na zamani.

“Don inganta harkokin gwamnati, nan ba da jimawa ba za mu bayyana tsare-tsaren mu na zamanantar da duk ayyukan gwamnati da kuma sake fasalin ma’aikatan, don aiwatar da tsarin tafiyar da harkokin gwamnati na zamani.

“Wannan zai haɗa da sabbin hanyoyin tantance ayyukan ma’aikata, horarwa da tabbatar da ƙwarewarsu a tsakanin wasu tsare-tsare da dama.

Ma'aikata

“Hakazalika, gwamnati ta ƙuduri aniyar hana zamba da wasu munanan ɗabi’un da suke gurɓata ayyukan gwamnati.

“Saboda sadaukarwar da ma’aikata suka yi a lokacin hidimarsu, ya dace a riƙa girmama su da mutunta su. Wannan ne ya sa muka ɗauki matakin biyan bashin garatuti da gwamnatinmu ta gada. Da zarar mun kawar da basukan, za mu tabbatar da biyan duk waɗanda suka yi ritaya daga ayyukan gwamnati da na ƙananan hukumomi cikin gaggawa.

Ma'aikata

“Da wannan aiki, In Sha Allahu, ma’aikata ba za su sake samun wani dalilin da zai sa su ji shakkar yin ritaya ba, wanda yakan haifar da kwaɗayin ci gaba da aiki.” In ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2024Albashin ma'aikataBikin Ranar Ma'aikataGwamna Dauda LawalZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanin Sin Ya Bayar Da Tallafin Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliya Ta Shafa A Kenya

Next Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mutane A Katsina Da Filato

Related

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata
Labarai

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

1 hour ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

4 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

6 hours ago
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa
Labarai

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

7 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

8 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

9 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'adda, Sun Ceto Mutane A Katsina Da Filato

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

May 14, 2025
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

May 14, 2025
Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

May 14, 2025
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

May 14, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 239, Sun Ƙwato Makamai Da Alburusai A Kogi

May 14, 2025
Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.