• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Ma’aikata: NLC Ta Bukaci Daidaita Albashin Ma’aikata A Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Ranar Ma’aikata: NLC Ta Bukaci Daidaita Albashin Ma’aikata A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Kwadago ta Kasa (NLC) a Jihar Kebbi, ta yi kira ga gwamnan jihar, Abubakar Atiku Bagudu, da ya aiwatar da tsarin daidaita albashin ma’aikata mafi karancin na N30,000 ga ma’aikatan jihar.

Shugaban kungiyar na jihar, Kwamared Murtala Usman, ne ya yi kiran a yayin jawabinsa na ranar bikin ma’aikata na bana a masaukin shugaban kasa da ke a Birnin Kebbi, ya ce bikin zagayowar ranar ma’aikata ita ce mai taken “Aiki mai fa’ida ga mata da maza a cikin yanayi na ‘yanci, daidaito, tsaro da mutuncin dan Adam”, a zahiri, ana daukar aiki da kyau idan: ana biyan ma’aikata kudaden albashi a kan gaskiya.

  • Ding Liren Ya Yi Nasara Kan Nepomniachtchi Inda Ya Zamo Basine Dan Wasan Dara Na Farko Da Ya Lashe Gasar Duniya
  • Motar Da Ta Kwaso Daliban Nijeriya Daga Sudan Ta Kama Da Wuta

Ya kara da cewa an ba da tabbacin aiki kuma akwai yanayin aiki lafiya; akwai daidaitattun dama da magani ga kowa; akwai kariyar zamantakewa ga ma’aikata da kuma iyalansu; akwai tsammanin ma’aikata don habaka kansu da kuma idan yana karfafa hafin gwiwar zamantakewa; ana barin ma’aikata cikin ‘yanci don bayyana damuwarsu kuma su tsara. Dangane da bayanan da ke sama muna da bukatu kamar haka: daidaitawa tsarin fansho kashi uku da muke da shi wanda ya kasance 12%, 15.5% da 33% da aiwatar da kashi 30% daidaitaccen sakamako.

Haka kuma ya ce, kungiyar ma’aikatan jinya da ungozoma a jihar na fatan gabatar da bukatarsu don yin la’akari da yiwuwar aiwatar da su Alawus alawus ga duk ma’aikatan jinya da ungozoma a fadin jihar, cikakkun aiwatar da tsarin albashin CONHESS, inganta tsaro don bai wa ma’aikatan jinya da ungozoma damar gudanar da ayyukansu na doka musamman a yankunan da ke fama da matsalar rashin tsaro, sai dai daidaita albashi ga malamai a kwalejin kimiyyar jinya da sauran batutuwa.

A cewar shugaban, akwai bukatar a yi la’akari da yadda ake gudanar da nade-naden mukamai a ma’aikatar jihar, kamar shugaban ma’aikatan gwamnati, sakatarorin dindindin da sauran wadanda suka dade su na rike da mukamai na rikon kwarya. Hakazalika da daidaita nade-naden nasu zuwa manyan mukamai zai taimaka matuka wajen inganta ayyukan ma’aikatan Jihar Kebbi.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Shugaban kungiyar NLC, ya yi nuni da cewa, taken ranar Ma’aikata na shekara ta 2023 wanda shi ne “Hakkin ma’aikata da adalci na zamantakewar al’umma” na da shakku ganin yadda ake tauye hakkin ma’aikata a wuraren aiki da kuma a jihohi da dama a fadin kasar nan. Yana da kyau a lura da cewa tauye hakkin ma’aikata na iya haifar da hana musu adalci na zamantakewa da tattalin arziki, a wurare da yawa na aiki, mahimman abubuwan da ke da mahimmanci don samun kyakkyawan aiki, wanda yana daya daga cikin hakkin ma’aikata masu aiki ba su bayar ba.

Daga bisa sun mika godiya da jinjina wa gwamna Abubakar Atiku Bagudu bisa biyan kudin gratuti da kuma cikin hakkin ma’aikatan Jihar Kebbi.

A nasa jawabin, Gwamna Abubakar Atiku Bagudu, ya ce “Na lura da dukkan bukatar da shugaban Kwadago na jiha, Kwamared Murtala Usman ya gabatar da kuma kiran da ake yi na a rika nada mukamai zuwa kwakkwaran aiki.’

Ya kuma ba da tabbacin ga ma’aikata don yin la’akari da aiwatar da su. Haka kuma Gwamnan ya yi karin bayani kan biyan kashi 40% na kwanan nan da gwamnatin tarayya ta amince da shi ga ma’aikata a matakin tarayya, ya kamata kungiyar kwadago ta fahimci cewa ba karin albashi ba ne don kaucewa haifar da wata muhawara tsakanin su da gwamnati a nan gaba kadan.

Gwamnan, ya kara da cewa amincewar ta kasance don daidaita albashin ma’aikata don daidaitawa da ma’aikatan da aka bar su a baya na ma’auni guda.

Ya kuma shawarci shugabannin kungiyar da su fara tunanin mafita da yadda za su jagoranci muhawara kan batun tallafin man fetur, domin nan ba da jimawa ba gwamnatinmu ba za ta iya ci gaba da biyan tallafin man fetur ba saboda muna fatara da tallafin mai a kasar nan, inji shi.

Bugudu, ya bayyana jin dadinsa da kyakkyawar alakar da ke tsakaninta da daukacin kungiyar kwadago a jihar, inda ya bukace su da su yi irin wannan aikin ga gwamnati mai zuwa, yayin da ya ce “Na biya kungiyar kwadagon bisa ga goyon bayan da na bayar ga wani mamban na tabbatar da cewa na tsayar da shi dan takarar gwamna don ya gaje ni, ya kuma lashe zabe yanzu shi ne wanda zai gade ni”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlbashiBaguduKebbiNlcRanar Ma'aikata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Majalisar Dokokin Zimbabwe: Ba Za A Amince Da Leken Asirin Da Amurka Ta Yi Wa Babban Sakataren MDD Ba

Next Post

Ina Da Yakinin Samun Nasara A Kotu -Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

5 hours ago
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
Labarai

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

6 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

8 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

10 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

12 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

13 hours ago
Next Post
Ina Da Yakinin Samun Nasara A Kotu -Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi

Ina Da Yakinin Samun Nasara A Kotu -Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.