• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Tunawa Da Mazan Jiya: Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Inganta Rayuwar Iyalan Jaruman Da Suka Rasu

by Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Ranar Tunawa Da Mazan Jiya: Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Inganta Rayuwar Iyalan Jaruman Da Suka Rasu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na inganta jin daɗin iyalan hafsoshi da suka rasa rayukansu a bakin aiki.

 

Gwamnan ya halarci bikin tunawa da sojojin da suka rasu a ranar Laraba a harabar baje kolin kasuwanci da ke Gusau, babban birnin jihar.

  • Da Ɗumi-ɗumi: Sojoji Sun Haramta Amfani Da Jirage Marasa Matuƙa A Arewa Maso Gabas
  • Karramawa: Ma’aikatan Kano Sun Yaba Wa Jagorancin Gwamna Abba Na Tausayi

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta bayyana cewa Gwamna Daudaa Lawal ya bayar da gudunmawar Naira miliyan 20 ga Rundunar Sojojin Nijeriya, reshen Jihar Zamfara a yayin ƙaddamar da tambarin tunawa da sojojin da suka rasu na shekarar 2025.

 

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

Sanarwar ta ƙara da cewa, gwamnan ya duba wani tambari da rundunar sojin Nijeriya suka ɗora. “Gwamna Lawal shi ma ya jagoranci shimfiɗa furannin sannan ya ba da umarnin a yi shiru na minti ɗaya domin karrama jaruman da suka rasu.”

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya jaddada cewa yau ranar tunawa da jaruman da suka mutu ne, kuma kira ne ga ɗaukacin al’ummar jihar Zamfara da ma kasa baki ɗaya.

 

“Ana yi bikin tunawa da sojojin Nijeriya ne a duk faɗin ƙasar a ranar 15 ga watan Junairu na kowace shekara domin tunawa da kuma jinjina wa waɗanda suka sadaukar da ransu da tsofaffin sojojinmu da suka yi fafutuka wajen kare martabar yankin Nijeriya, waɗanda suka sadaukar da rayuwarsu domin mu samu damar zama lafiya.

 

“Muna godiya kuma muna daraja sadaukarwar da suka yi, wanda ya kawo sauyi a rayuwarmu a yau. Tare da godiya da mutuntawa, mun yi alƙawarin ci gaba da tunawa da su tare da tallafa wa iyalan ​​da suka bari.

 

“Wannan rana ta zama karramawa ga jaruman mu da suka mutu da kuma kira ga ɗaukacin al’ummar jihar Zamfara da ma kasa baki ɗaya. Wata dama ce ta yin tunani a kan sadaukarwar da waɗancan jajirtattun mutane suka yi. Ya kamata sadaukarwar sojojinmu ya zaburar da mu wajen habaka zaman lafiyar da muka samu a yau da kuma fafutukar samar da gobe mai kyau.

 

“Kada mu manta da muhimmancin tallafa wa iyalan waɗannan jarumai da suka mutu da kuma tsofaffin da suka yi yaƙi domin mu yi barci cikin lumana da kuma waɗanda har yanzu suke da rauni na hidimar da suke yi wa ƙasa. Juriya da sadaukarwarsu dole ne ya tunatar da mu alhakin da ya rataya a wuyanmu na tabbatar da jin daɗinsu. Ta yin haka, muna girmama sadaukarwar da suka yi, kuma muna nuna godiyarmu ga jajircewar da suke yi ga al’ummarmu.”

 

Gwamnan ya bayyana cewa, duk da ƙarancin kayan aiki, ana samun gagarumin ci gaba wajen magance matsalolin tsaron cikin gida ta jihar ta hanyoyi daban-daban.

 

“Wannan gwamnatin ba wai kawai ta ba da tallafin kayan aiki masu muhimmanci ba ne. Har ila yau, ta kuma tabbatar da jin daɗin iyalan jami’an da suka rasa rayukansu a bakin aiki. Mun himmatu wajen biyan kuɗaɗen jinya ga waɗanda suka jikkata a ayyukan tsaro da tallafa wa jaruman mu da iyalansu.

 

“A wani bangare na ƙoƙarin da gwamnatina ke yi na daƙile matsalolin tsaro, mun samar da motocin tsaro sanye da na’urori na zamani, tare da babura ga jami’an tsaro. Wannan yunƙurin na ƙara haɓaka damarsu ta hanyar shiga wurare masu rintsi don tabbatar da cewa babu wani yanki na jiharmu da ke a baya.

 

“Muna ci gaba da jajircewa wajen ƙarfafa dabarun haɗin gwiwa tare da jihohi makwabta, hukumomin tsaro, da sauran masu ruwa da tsaki don tunkarar ƙalubalen tsaro da ke addabar jiharmu, domin haɗin gwiwa shi ne babban jigon samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Samu Kyakkyawan Sakamako A Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Sauran Kasashe A 2024

Next Post

Sin Ta Kara Wasu Kamfanonin Amurka 7 Cikin Jerin Sassan Da Ba Za A Iya Dogaro Da Su Ba

Related

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

2 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

4 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

5 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

6 hours ago
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
Labarai

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

8 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

9 hours ago
Next Post
Sin Ta Kara Wasu Kamfanonin Amurka 7 Cikin Jerin Sassan Da Ba Za A Iya Dogaro Da Su Ba

Sin Ta Kara Wasu Kamfanonin Amurka 7 Cikin Jerin Sassan Da Ba Za A Iya Dogaro Da Su Ba

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.