ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Tunawa Da Mazan Jiya: Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Inganta Rayuwar Iyalan Jaruman Da Suka Rasu

by Sulaiman
10 months ago
Mazan jiya

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na inganta jin daɗin iyalan hafsoshi da suka rasa rayukansu a bakin aiki.

 

Gwamnan ya halarci bikin tunawa da sojojin da suka rasu a ranar Laraba a harabar baje kolin kasuwanci da ke Gusau, babban birnin jihar.

ADVERTISEMENT
  • Da Ɗumi-ɗumi: Sojoji Sun Haramta Amfani Da Jirage Marasa Matuƙa A Arewa Maso Gabas
  • Karramawa: Ma’aikatan Kano Sun Yaba Wa Jagorancin Gwamna Abba Na Tausayi

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta bayyana cewa Gwamna Daudaa Lawal ya bayar da gudunmawar Naira miliyan 20 ga Rundunar Sojojin Nijeriya, reshen Jihar Zamfara a yayin ƙaddamar da tambarin tunawa da sojojin da suka rasu na shekarar 2025.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Sanarwar ta ƙara da cewa, gwamnan ya duba wani tambari da rundunar sojin Nijeriya suka ɗora. “Gwamna Lawal shi ma ya jagoranci shimfiɗa furannin sannan ya ba da umarnin a yi shiru na minti ɗaya domin karrama jaruman da suka rasu.”

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya jaddada cewa yau ranar tunawa da jaruman da suka mutu ne, kuma kira ne ga ɗaukacin al’ummar jihar Zamfara da ma kasa baki ɗaya.

 

“Ana yi bikin tunawa da sojojin Nijeriya ne a duk faɗin ƙasar a ranar 15 ga watan Junairu na kowace shekara domin tunawa da kuma jinjina wa waɗanda suka sadaukar da ransu da tsofaffin sojojinmu da suka yi fafutuka wajen kare martabar yankin Nijeriya, waɗanda suka sadaukar da rayuwarsu domin mu samu damar zama lafiya.

 

“Muna godiya kuma muna daraja sadaukarwar da suka yi, wanda ya kawo sauyi a rayuwarmu a yau. Tare da godiya da mutuntawa, mun yi alƙawarin ci gaba da tunawa da su tare da tallafa wa iyalan ​​da suka bari.

 

“Wannan rana ta zama karramawa ga jaruman mu da suka mutu da kuma kira ga ɗaukacin al’ummar jihar Zamfara da ma kasa baki ɗaya. Wata dama ce ta yin tunani a kan sadaukarwar da waɗancan jajirtattun mutane suka yi. Ya kamata sadaukarwar sojojinmu ya zaburar da mu wajen habaka zaman lafiyar da muka samu a yau da kuma fafutukar samar da gobe mai kyau.

 

“Kada mu manta da muhimmancin tallafa wa iyalan waɗannan jarumai da suka mutu da kuma tsofaffin da suka yi yaƙi domin mu yi barci cikin lumana da kuma waɗanda har yanzu suke da rauni na hidimar da suke yi wa ƙasa. Juriya da sadaukarwarsu dole ne ya tunatar da mu alhakin da ya rataya a wuyanmu na tabbatar da jin daɗinsu. Ta yin haka, muna girmama sadaukarwar da suka yi, kuma muna nuna godiyarmu ga jajircewar da suke yi ga al’ummarmu.”

 

Gwamnan ya bayyana cewa, duk da ƙarancin kayan aiki, ana samun gagarumin ci gaba wajen magance matsalolin tsaron cikin gida ta jihar ta hanyoyi daban-daban.

 

“Wannan gwamnatin ba wai kawai ta ba da tallafin kayan aiki masu muhimmanci ba ne. Har ila yau, ta kuma tabbatar da jin daɗin iyalan jami’an da suka rasa rayukansu a bakin aiki. Mun himmatu wajen biyan kuɗaɗen jinya ga waɗanda suka jikkata a ayyukan tsaro da tallafa wa jaruman mu da iyalansu.

 

“A wani bangare na ƙoƙarin da gwamnatina ke yi na daƙile matsalolin tsaro, mun samar da motocin tsaro sanye da na’urori na zamani, tare da babura ga jami’an tsaro. Wannan yunƙurin na ƙara haɓaka damarsu ta hanyar shiga wurare masu rintsi don tabbatar da cewa babu wani yanki na jiharmu da ke a baya.

 

“Muna ci gaba da jajircewa wajen ƙarfafa dabarun haɗin gwiwa tare da jihohi makwabta, hukumomin tsaro, da sauran masu ruwa da tsaki don tunkarar ƙalubalen tsaro da ke addabar jiharmu, domin haɗin gwiwa shi ne babban jigon samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna
Manyan Labarai

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba
Manyan Labarai

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Coas
Manyan Labarai

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Next Post
Sin Ta Kara Wasu Kamfanonin Amurka 7 Cikin Jerin Sassan Da Ba Za A Iya Dogaro Da Su Ba

Sin Ta Kara Wasu Kamfanonin Amurka 7 Cikin Jerin Sassan Da Ba Za A Iya Dogaro Da Su Ba

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.