ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Tunawa Da Mazan Jiya: Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Inganta Rayuwar Iyalan Jaruman Da Suka Rasu

by Sulaiman
1 year ago
Mazan jiya

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na inganta jin daɗin iyalan hafsoshi da suka rasa rayukansu a bakin aiki.

 

Gwamnan ya halarci bikin tunawa da sojojin da suka rasu a ranar Laraba a harabar baje kolin kasuwanci da ke Gusau, babban birnin jihar.

ADVERTISEMENT
  • Da Ɗumi-ɗumi: Sojoji Sun Haramta Amfani Da Jirage Marasa Matuƙa A Arewa Maso Gabas
  • Karramawa: Ma’aikatan Kano Sun Yaba Wa Jagorancin Gwamna Abba Na Tausayi

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta bayyana cewa Gwamna Daudaa Lawal ya bayar da gudunmawar Naira miliyan 20 ga Rundunar Sojojin Nijeriya, reshen Jihar Zamfara a yayin ƙaddamar da tambarin tunawa da sojojin da suka rasu na shekarar 2025.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sanarwar ta ƙara da cewa, gwamnan ya duba wani tambari da rundunar sojin Nijeriya suka ɗora. “Gwamna Lawal shi ma ya jagoranci shimfiɗa furannin sannan ya ba da umarnin a yi shiru na minti ɗaya domin karrama jaruman da suka rasu.”

 

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya jaddada cewa yau ranar tunawa da jaruman da suka mutu ne, kuma kira ne ga ɗaukacin al’ummar jihar Zamfara da ma kasa baki ɗaya.

 

“Ana yi bikin tunawa da sojojin Nijeriya ne a duk faɗin ƙasar a ranar 15 ga watan Junairu na kowace shekara domin tunawa da kuma jinjina wa waɗanda suka sadaukar da ransu da tsofaffin sojojinmu da suka yi fafutuka wajen kare martabar yankin Nijeriya, waɗanda suka sadaukar da rayuwarsu domin mu samu damar zama lafiya.

 

“Muna godiya kuma muna daraja sadaukarwar da suka yi, wanda ya kawo sauyi a rayuwarmu a yau. Tare da godiya da mutuntawa, mun yi alƙawarin ci gaba da tunawa da su tare da tallafa wa iyalan ​​da suka bari.

 

“Wannan rana ta zama karramawa ga jaruman mu da suka mutu da kuma kira ga ɗaukacin al’ummar jihar Zamfara da ma kasa baki ɗaya. Wata dama ce ta yin tunani a kan sadaukarwar da waɗancan jajirtattun mutane suka yi. Ya kamata sadaukarwar sojojinmu ya zaburar da mu wajen habaka zaman lafiyar da muka samu a yau da kuma fafutukar samar da gobe mai kyau.

 

“Kada mu manta da muhimmancin tallafa wa iyalan waɗannan jarumai da suka mutu da kuma tsofaffin da suka yi yaƙi domin mu yi barci cikin lumana da kuma waɗanda har yanzu suke da rauni na hidimar da suke yi wa ƙasa. Juriya da sadaukarwarsu dole ne ya tunatar da mu alhakin da ya rataya a wuyanmu na tabbatar da jin daɗinsu. Ta yin haka, muna girmama sadaukarwar da suka yi, kuma muna nuna godiyarmu ga jajircewar da suke yi ga al’ummarmu.”

 

Gwamnan ya bayyana cewa, duk da ƙarancin kayan aiki, ana samun gagarumin ci gaba wajen magance matsalolin tsaron cikin gida ta jihar ta hanyoyi daban-daban.

 

“Wannan gwamnatin ba wai kawai ta ba da tallafin kayan aiki masu muhimmanci ba ne. Har ila yau, ta kuma tabbatar da jin daɗin iyalan jami’an da suka rasa rayukansu a bakin aiki. Mun himmatu wajen biyan kuɗaɗen jinya ga waɗanda suka jikkata a ayyukan tsaro da tallafa wa jaruman mu da iyalansu.

 

“A wani bangare na ƙoƙarin da gwamnatina ke yi na daƙile matsalolin tsaro, mun samar da motocin tsaro sanye da na’urori na zamani, tare da babura ga jami’an tsaro. Wannan yunƙurin na ƙara haɓaka damarsu ta hanyar shiga wurare masu rintsi don tabbatar da cewa babu wani yanki na jiharmu da ke a baya.

 

“Muna ci gaba da jajircewa wajen ƙarfafa dabarun haɗin gwiwa tare da jihohi makwabta, hukumomin tsaro, da sauran masu ruwa da tsaki don tunkarar ƙalubalen tsaro da ke addabar jiharmu, domin haɗin gwiwa shi ne babban jigon samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.”

Mazan jiya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Sin Ta Kara Wasu Kamfanonin Amurka 7 Cikin Jerin Sassan Da Ba Za A Iya Dogaro Da Su Ba

Sin Ta Kara Wasu Kamfanonin Amurka 7 Cikin Jerin Sassan Da Ba Za A Iya Dogaro Da Su Ba

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.