• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Yaki Da Cizon Sauro: Majalisa Ta Bukaci Gwamnati Ta Ayyana Dokar Ta-baci Kan Malaria

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Ranar Yaki Da Cizon Sauro: Majalisa Ta Bukaci Gwamnati Ta Ayyana Dokar Ta-baci Kan Malaria
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Wakilai ta tarayya ta bukaci gwamnatin tarayya ta ayyana dokar ta-baci kan cutar maleriya, tare da misalta cutar a matsayin mai mummuke mutane sannu a hankali da ke janyo mutuwan ‘yan Nijeriya.

Shugaban kwamitin yaki da cutar zazzabin cikin sauro, tarin fuka, da cutar nan mai karya garkuwar jiki wato (HIV), na majalisar, Hon. Amobi Ogah, shi ne ya shaida hakan ta cikin sanarwar da ya fitar ga ‘yan jarida a Abuja ranar Lahadi domin raya bikin ranar yaki da cizon sauro ta duniya na 2023.

  • Cutar Maleriya Ta Kashe Mutum 290,000 A Duniya A Cikin Shekara Biyu

Ana raya bikin yaki da cizon sauro ne a duk duniya a duk ranar 20 ga watan Agusta domin nazari da bibiyar hanyoyin dakile kisan da cizon sauro ke yi wa jama’a.

Manufar da ke cikin hakan shi ne domin wayar da kan jama’a da kuma daukan matakan kariya daga cutar tare da jawo hankalin hukumomi wajen daukan matakan da suka dace domin shawo kan cutar maleriya da ke addabar jama’a.

Ogah, dan majalisar mai wakiltar mazabar Isuiwuato/Umunneochi daga jihar Abia, ya ce, maleriya ta zama babban barazana ga kiwon lafiya, kuma akwai bukatar daukan dukkanin matakan dakile yawan mutuwa da ake yi a sanadiyyar cutar.

Labarai Masu Nasaba

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

TRCN Ta Koka Kan Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya 

Ya ce, majalisar ta 10 za ta yi dukkanin mai yiyu wajen ganin an rage kaifin illar da cutar maleriya ke yi a Nijeriya.

“Kwamitinmu za ta yi aiki da hukumomin da suka dace wajen yaki da cutar maleriya kuma za mu tabbatar dukanin kudin da aka ware an yi amfani da su domin tabbatar da cimma manufar da ake so.

“A cewar hukumar lafiya ta duniya, kasashen Afrika hudu sune ke da rinjayen masu mutuwa sakamakon cutar maleriya. Nijeriya kuma ita ce ke kan gaba da kaso 31.3 cikin dari, yayin da jamhuriyyar Congo take biye mata da kaso 12.6 cikin dari sai kuma, Tanzania mai kaso 4.1, yayin da jamhuriyyar Nijar take da kaso 3.9 cikin dari.”

Ya ce, Nijeriya na bukatar kariya daga cutar malaria. Ya bukaci gwamnati da masu ruwa da tsaki da su tabbatar sun rage kaifin yaduwar cutar maleriya tare da kare jama’a daga illar da zazzabin cizon sauro ke janyowa.

Dan majalisar ya ce dukkanin kokarin da ya dace a yi wajen kawar da cutar maleriya ya kamata a yi hakan domin kula da kiwon lafiyan al’ummar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cizon sauroZazzabin Cizon Sauro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Tinubu Ya Sauya Wa Momoh, Oyetola, Alkali, Tunji-Ojo Ma’aikatu

Next Post

Jami’ar Edo Ta Kori Ma’aikata 5, Wasu 21 Na Fuskantar Bincike Kan Aikata Manyan Laifuka

Related

Tinubu
Manyan Labarai

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

33 minutes ago
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)
Labarai

TRCN Ta Koka Kan Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya 

2 hours ago
Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba

3 hours ago
Kwale-kwale
Labarai

Kifewar Kwale-kwale, Ya Ci Rayukan ‘Yan Uwa 5 A Benuwe 

5 hours ago
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu
Manyan Labarai

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

8 hours ago
Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara
Tsaro

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

17 hours ago
Next Post
Jami’ar Edo Ta Kori Ma’aikata 5, Wasu 21 Na Fuskantar Bincike Kan Aikata Manyan Laifuka

Jami’ar Edo Ta Kori Ma’aikata 5, Wasu 21 Na Fuskantar Bincike Kan Aikata Manyan Laifuka

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

October 6, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

TRCN Ta Koka Kan Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya 

October 6, 2025
Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar

Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar

October 6, 2025
Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba

Sojoji Sun Tarwatsa Maɓoyar ‘Yan Bindiga 11, Sun Ƙwato Makamai A Taraba

October 6, 2025
Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

October 6, 2025
Kwale-kwale

Kifewar Kwale-kwale, Ya Ci Rayukan ‘Yan Uwa 5 A Benuwe 

October 6, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

October 6, 2025
Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.