• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Ilimin Iyaye Na Haifar Da Karuwar Yaran Da Ba Su Zuwa Makaranta (2)

by Idris Aliyu Daudawa
10 months ago
in Ilimi
0
Rashin Ilimin Iyaye Na Haifar Da Karuwar Yaran Da Ba Su Zuwa Makaranta (2)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sauran abubuwan da suke taimakawa kamar yadda ya yi bayani masu matukar muhimmanci sune mutane masu zaman kansu, hukumomi,sai kuma ga shi basu taimakawa kokarin da gwamanati kamar yadda ya dace, saboda ita kadai ba zata iya tafiyar da lamarin ilimi ba.

Ya yi kira da abokan tafiya na kasa da kasa da sauran masu zaman kansu su taimakawa gwamnati ta wajen daukar nauyin masu taimakawa,cigaba da aiki dasu,da irin aibashin da za a rika ba masu taimakawar.

  • Masu Zanga-zanga Sun Fito Duk Da Dokar Hana Fita A Jigawa
  • Zanga-Zanga Ta Yi Sanadin Ɓarna Mai Yawa A Jigawa, An Sanya Dokar Hana Fita

Saboda yawancinsu duk malaman makaranta ne,suna bangare na ilimi.Hakanan ma yawancin gwamnatocin Jihohi basu maida hankalinsu ba wajen daukar aiki na masu taimakawa da kuma ci gaba da tafiya tare.Shi yasa duk yadda aka kalli lamarin yaki da jahilci bada gaske ake ba,musamman ma idan aka dubi yadda kowa zai iya taimakawa.

Masanin ilimi, Micheal Ojonugwa, cewa ya yi babbar matsalar da ake fuskanta wajen kokarin da ake da yaki da jahilci shine yawan wadanda basu da ilimi matsalar yaran da basu zuwa makaranta a Nijeriya.

Ya jaddada idan har ana da matasa da manya masu yawa da suke da ilimi su da kansu za suyi kokarin ganin sai ‘ya’yansu ko ‘yan’uwansu sai sun sa su makaranta,da haka ne kuma kokarin nasu zai rage yawan yara wadanda basu zuwa makaranta.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

Akwai dalilai masu yawa wadanda suka kasance wani tarnaki akan yawan wadanda basu da ilimi,babba daga cikinsu shine yawancin iyaye suna fama da talauci, lamarinsu bai wuce abinda za su ci ba,babu wata maganar zuwa makaranta.

Ojonugwa kamar yadda ya kara jaddadawa matsalar da tafim cimma al’umma tuwo a kwarya al’umma ita ce matsalar tsaron da ake f ama da a Nijeriya, inda dalibai da malamai a makaranta ake masu Kallon wadndaza a iya daukewa ayi garkuwa dasu har ma da kashewa. Wannan shi yake sa was uke cewa yafi dacewa su tsaya gida maimakon a dauke su da sunan neman ilimi.

Kamar yadda yace: “fifikon da ake da shi tsakanin tsakanin wannan sashen da wancan da akwai bukatar a dauki mataki cikin gaggawa a wuraren da karanci wadanda suka yaki jahilci.Maganar gaskiya idan har za a samu damar kara yawan masu ilimi sannu a hankali lamarin rashin tsaro watarana zai zama tarihi,saboda yawancin wadanda ake amfani dasu basu da ilimi ne da kuma muaten da suke ganin an maida su saniyar ware.”

Yayin da yake cewa lamarin mizanin masu ilimi ya kamata ace an wuce inda ake a yanzu kamar yadda ya ce ‘’ amma kuma Nijeriya tana fama da matsalar rashin tsaro, fatara,da sauran matsaloli, abin so ne aga cewar an yi maganin matsalolin kafin a samu wani cigaba kan lamarin da ya shafi karuwar masu mizanin masu ilimi.”

Wani jami’ar ilimi wadda take kulawa da lamarin daya shafi yaki da jahilci a wasu cibiyoyi na Abuja amma bata son a ambaci sunanta,tace yawancin cibiyoyi ba masu zuwa da yawa, domin su yaki jahilci,saboda ba a wayar da mutane ba, basu san abinda ake ba, basu sanin muhimmancin mutumin da ya kasance mai ilimi ba.

Ta ce yawancin manya yanzu suna maida hankali ne a lamarin kasuwanci da wasu ayyukan da basu taka nkara sun karya ba, maimakon zuwa makaranta.

“Amma kuma ba za a ga laifinsu ba saboda fatara ko talauci suna damuwar kowa a Nijeriya, ya kuma kamata mutane su ci abinci tukuna kafin su dauki mataki kan wani abinda suke son yi kamar yadda dace,”.

Gwamnatoci na daban- dabn ya dace su zuba jari sosai a bangaren ilimin yaki da jahilci idan har ana son samun cigaban ilimi a Nijeriya, yayin da take ga masu hannu da shuni su taimaka wajen kara bunkasa sashen domin ya bunkasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IlimiIyayeYara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ka Kalli Kanka Ka Ga Ka Fi Karfin Bukatunka Babbar Nasara Ce – Khadija Abdullahi

Next Post

Ƴansanda Sun Fara Bi Gida-Gida Don Ƙwato Kayan Da Aka Sace Yayin Zanga-Zanga A Kano

Related

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

5 days ago
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum
Ilimi

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

6 days ago
Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara
Ilimi

Bayan Biyan Basussuka: WAEC Da NECO Sun Saki Samakon Jarrabawar Jihar Zamfara

6 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (3)

6 days ago
Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu
Ilimi

Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)
Ilimi

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)

2 weeks ago
Next Post
Ƴansanda Sun Fara Bi Gida-Gida Don Ƙwato Kayan Da Aka Sace Yayin Zanga-Zanga A Kano

Ƴansanda Sun Fara Bi Gida-Gida Don Ƙwato Kayan Da Aka Sace Yayin Zanga-Zanga A Kano

LABARAI MASU NASABA

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.