• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Ingantaccen Shugabancin Siyasa Ne Silar Wahalhalun Da Ake Fama Da Su A Nijeriya – Ezekwesili

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Ezekwesili

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohowar ministar ilimi, Dakta Obiageli Ezekwesili ta bayyana cewa rashin ingantaccen shugabancin siyasa ne silar wahalhalun tattalin arzikin da ake fama da su a Nijeriya.

Ezekwesili ta bayyana hakan ne wajen wani taro, inda ta yi kira a yi kokarin sauya tsarin mulki da siyasa da tsarin zabe da kuma tattalin arzikin kasar nan.

  • An Nuna Dandanon Shirye-Shiryen Bikin Sabuwar Shekarar Sinawa Na CMG A Filin Jiragen Sama Da Yankunan Kasuwanci Na Dubai
  • Ina Da Labarin Sirri ‘Yan Bindiga Za su Kawo Mun Farmaki – Gwamna Dikko Raɗɗa

Ta ce idan ana bukatar ci gaba dole ne ‘yan Nijeriya da sauren kasashen Afirka su sami ingantacciyar shugabancin siyasa.

Ezekwesili ta bayyana wa mahalarta taron cewa gazawar kasa ya ta’allaka ne ga irin shugabancin ko yadda ake mulkar mutane da kuma yadda ake tafiyar da albarkatun kasa ba ta hanyar kashin kai ba sai dai ta yadda zai inganta rayuwar al’umma.

Ta lallai idan ba a dauki wasu matakai ba a Nijeriya babu abin da zai iya sauyawa ko nan da shekaru 2060 ne, dole ne a gyara yaddda ake gudanar da shugabancin siyasa a kasar nan. A cewarta, ‘yan siyasar kasashen Afirka ba sa iya gudanar da tsarkakken shugabancin tsakanin su da mutane.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

A kan haka ne, Ezekwesili ta yi kira da a samar da sabuwar kungiya da za ta iya mamaye fagen siyasar Nijeriya da za ta hada masu kima da ka iya sauya alkiblar siyasar Nijeriya.

Ta kara da cewa akwai bukatar samar da sabon tsari ta hanyar horar da ‘yan Nijeriya a bangaren siyasa da kuma tsare-tsarin harkokin mulki ga wadanda aka bai wa sabbin mukamai domin sanin makaman aiki da za su kadada wa al’ummar da suke mulka. Sannan ta ce akwai bukatar ‘yan Nijeriya su hada kai tare da yin aiki kafada da kafada domin samun damar kyara kundin tsarin mulki da siyasa da harkokin zabe da kuma habaka tattalin arzin kasar nan.

“’Yan Nijeriya ne kawai za su iya aiki kafada da kafada domin tilasta wa bangarorin gwamnati uku tare da mayar da martanin gaggawa wajen dakile durkushewar kasar nan. Nijeriya ce kasa ta 13 a jerin kasashen duniya da suka gaza,” in ji ta.

A nasa bangaren, Farfesa a Jami’ar Stanford da ke kasar Amurka, Larry Diamond ya yi Allah wadai da yadda jam’iyyar mai mulki ke mamaye siyasar kasa da harkokin zabe har ya hana gudanar da sahihin zabe a kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Adawa Ne Suka Tunzura Mutane Yin Zanga-zanga A Neja Da Kano – APC

Next Post

Dalibai Miliyan 15.9 Ke Kashe Naira Biliyan 159 Duk Wata A Sayen Data

Related

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

14 minutes ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

1 hour ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

2 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

3 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

4 hours ago
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci
Addini

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

5 hours ago
Next Post
Data

Dalibai Miliyan 15.9 Ke Kashe Naira Biliyan 159 Duk Wata A Sayen Data

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.