• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Ingantaccen Shugabancin Siyasa Ne Silar Wahalhalun Da Ake Fama Da Su A Nijeriya – Ezekwesili

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Ezekwesili

Tsohowar ministar ilimi, Dakta Obiageli Ezekwesili ta bayyana cewa rashin ingantaccen shugabancin siyasa ne silar wahalhalun tattalin arzikin da ake fama da su a Nijeriya.

Ezekwesili ta bayyana hakan ne wajen wani taro, inda ta yi kira a yi kokarin sauya tsarin mulki da siyasa da tsarin zabe da kuma tattalin arzikin kasar nan.

  • An Nuna Dandanon Shirye-Shiryen Bikin Sabuwar Shekarar Sinawa Na CMG A Filin Jiragen Sama Da Yankunan Kasuwanci Na Dubai
  • Ina Da Labarin Sirri ‘Yan Bindiga Za su Kawo Mun Farmaki – Gwamna Dikko Raɗɗa

Ta ce idan ana bukatar ci gaba dole ne ‘yan Nijeriya da sauren kasashen Afirka su sami ingantacciyar shugabancin siyasa.

Ezekwesili ta bayyana wa mahalarta taron cewa gazawar kasa ya ta’allaka ne ga irin shugabancin ko yadda ake mulkar mutane da kuma yadda ake tafiyar da albarkatun kasa ba ta hanyar kashin kai ba sai dai ta yadda zai inganta rayuwar al’umma.

Ta lallai idan ba a dauki wasu matakai ba a Nijeriya babu abin da zai iya sauyawa ko nan da shekaru 2060 ne, dole ne a gyara yaddda ake gudanar da shugabancin siyasa a kasar nan. A cewarta, ‘yan siyasar kasashen Afirka ba sa iya gudanar da tsarkakken shugabancin tsakanin su da mutane.

LABARAI MASU NASABA

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

A kan haka ne, Ezekwesili ta yi kira da a samar da sabuwar kungiya da za ta iya mamaye fagen siyasar Nijeriya da za ta hada masu kima da ka iya sauya alkiblar siyasar Nijeriya.

Ta kara da cewa akwai bukatar samar da sabon tsari ta hanyar horar da ‘yan Nijeriya a bangaren siyasa da kuma tsare-tsarin harkokin mulki ga wadanda aka bai wa sabbin mukamai domin sanin makaman aiki da za su kadada wa al’ummar da suke mulka. Sannan ta ce akwai bukatar ‘yan Nijeriya su hada kai tare da yin aiki kafada da kafada domin samun damar kyara kundin tsarin mulki da siyasa da harkokin zabe da kuma habaka tattalin arzin kasar nan.

“’Yan Nijeriya ne kawai za su iya aiki kafada da kafada domin tilasta wa bangarorin gwamnati uku tare da mayar da martanin gaggawa wajen dakile durkushewar kasar nan. Nijeriya ce kasa ta 13 a jerin kasashen duniya da suka gaza,” in ji ta.

A nasa bangaren, Farfesa a Jami’ar Stanford da ke kasar Amurka, Larry Diamond ya yi Allah wadai da yadda jam’iyyar mai mulki ke mamaye siyasar kasa da harkokin zabe har ya hana gudanar da sahihin zabe a kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 
Labarai

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Kotu
Manyan Labarai

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Asuu
Labarai

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Next Post
Data

Dalibai Miliyan 15.9 Ke Kashe Naira Biliyan 159 Duk Wata A Sayen Data

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
Asuu

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.