ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Kasuwa Da Cin Zarafi Na Cikin Manyan Kalubalen Kannywood – Sani Abubakar

by Rabilu Sanusi Bena
2 years ago
Kasuwa

LABARAI MASU NASABA

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Wannan ita ce karshen tattaunawa da Jarumi SANI ABUBAKAR da muka fara kawowa a makon da ya gabata tare da wakiliyarmu, RABI’AT SIDI BALA. A karanta har karshe don jin abubuwan ta kunsa kamar haka:

Tun daga farkon farawarka kawo yanzu wanne irin kalubale ka fuskanta cikin masana’antar?

Shi kalubale ba a rasa shi, a gaskiyar magana tun daga farko kawo yanzu ba zan iya cewa ga wani babban kalubale dana hadu da shi ba face rashin kasuwa, yadda sana’ar ta canja ba yadda take da farko ba akalarta ta juya ta yi canji kala-kala, wannan canji da ta kawo bangaren kasuwa shi ne kawai kalubalen. Sannan babban abin da ya fi damu na shi ne za ka ga mutum ya fito ya ci zarafinmu amma ba mu da ikon ramawa su ma shuwagabanninmu sai dai kawai su zuba ido saboda gudun kar mutum ya zo yayi magana wani ya fadi maganar da hankalinka ba zai iya dauka ba, gaskiya wadannan shi ne matsalolin da nake ganin su ka fi damuna. za ka ga mutumin da bai ma san ya sana’ar taka take ba, bai ma taba zuwa ya ga ya ma ake sana’ar ba, bai san ya aka fara ta ya ake kare ta ba, amma za ka ga ya fito yana cin mutunci, ko cin zarafi yana zaginku a cikin masana’antar, kuma karshe dai abu daya kawai za a yi a ce a yi hakuri. Babu wata masana’anta ko wajen sana’a da za ka tarar ana zagin mutum ko ana cin zarafinsa kuma babu yadda zai yi sai masana’antar Kannywood. Ni dai tunda nake cikin masana’antar babu wani wanda ya taba daukar wani tallafi ya ce ga wani tallafi an ba da domin ci gaban masana’antar in dai ba maigidana ba, na tabbatar sanata ya taimaki ‘yan kannywood wanda kuma duk abin da aka yi kusan da hannuna ma a ciki, amma kalubale na cin mutunci da cin zarafi dai muna gani.

Ba ka ganin wasun cikinku ne ke nemo muku zagin, ta yadda suke tafiyar da nasu al’amuran har ta kai da an yi muku kudin goro, ko ya abun yake?

Gaskiyar magana guda daya ita ce; duk cikin al’ummar da ki ka gani, kuma kowacce irin masana’anta a duniya dole akwai bata gari a cikinta kuma akwai na kirki, dan haka babu yadda za a ce mu wankakku ne dan muna wannan maganar, a’a! dole akwai bata gari a cikinmu. Amma maganar na ce wani ne yake janyo mana zagi a’a! ai bai kamata ka yi shari’a ba tare da, ka san me ye yake faruwa ba. Dole a cikin al’umma idan kana sana’a sai ka tarar da bata gari da zai ja maka zagi wannan kuwa mun sani, hatta a cikinku ‘yan jarida ku kun sani akwai wadanda bata gari ne suke ja muku zagi akan sana’arku, ba za ku ce ku a cikin sana’arku babu mai zaginku ba, a kowacce sana’a ana zagin mutane.

Na ji ka ce ba wanda ya taba ba ka wani tallafi a masana’antar, to ya batun kallon da sauran jama’a ke yi wa ‘yan kannywood na cewar; suna tafiya ne da gwamnati, yayin da jam’iyya tayi nasara tana ware musu wasu kudade na daban, me za ka ce akan hakan?

Gaskiyar magana shi dan fim zai iya yin siyasa, misali; kamar ni kin ga tunda nake da maigidana  nake tafiya tare da shi, ni ba jam’iyya nake bi ba, bayan zaben maigidana zan duba na ga wa ya cancanta na zabe shi?, kuma ni bana bin wani dan siyasa bayan maigidana, akwai masu yin hakan amma akwai wanda ba sa canja jam’iyya a ‘yan kannywood din. Kuma dole ai dan fim yayi siyasa saboda siyasa ta kowa ce dole ka duba ka ga ya za a yi al’ummarka ta zama gyararriyar al’umma?, misali; dole ka  duba ka hanga ka gani wane ne zai taimaki al’umma, inda gudunmawar da za ka ba shi kai ma ka bada taka irin gudunmawar, ni kin ga Barau Jibril Maliya ne maigidana, dan haka dole ina bin sa dan na tabbatar da cewa inada yakini dari bisa dari yana kyautatawa al’umma.

Ya batun nasarori fa, wanne irin nasarori ka samu game da fim?

Sai dai na ce Alhamdulillahi dan ban isa ma na ce ga iyakacinsu ba, an same su da yawa burjik kuma ana kan samu, dan cikin sana’ar Allah ya rufa ma asiri ai ka gama samun nasara, an samu nasarori babu iyaka gaskiya.

Kasuwa
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Next Post
Zan Bar Barcelona A Karshen Kakar Wasanni Ta Bana-Xavi

Zan Bar Barcelona A Karshen Kakar Wasanni Ta Bana-Xavi

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.