• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Shugabanni Na Kwarai Ke Kara Rura Matsalolin Arewa – Ibrahim Galadanci

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Rashin Shugabanni Na Kwarai Ke Kara Rura Matsalolin Arewa – Ibrahim Galadanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Gamayyar Kungiyoyin Matasan Arewa mazauna Jihar Legas, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci, ya bayyana cewar, rashin shugabanni na kwarai da ake fama da shi a Nijeriya na daga cikin manyan matsalolin da suke janyo koma baya ga Arewa.

Ya ce, hatta matsalolin tsaron da ake ta fama da su, rashin adilan shugabanni ne ke kara janyo matsalar, sai ya bukaci ‘yan Nijeriya musamman ‘yan Arewa da su yi amfani da lokacin zaben 2023 wajen zaban Shugabanni na kwarai da za su iya kyautata rayuwar al’umma.

  • Buhari Ya Jinjina Wa Portugal Kan Samar Da Tsaro A Afrika

“Wannan matsalar sakacin shugabanni ne domin ba mu da Shugabanni wadanda suke kokarin kare ‘yancin ‘yan Arewa ma baki daya, domin da muna da su da wadannan abubuwan ba za su ci gaba da faruwa ba don iyaka yankin arewa ake wannan abun.

“Dan arewa ba shi da ‘yancin zuwa gona ko kasuwa ko hawa hanya, yanzu ka duba tafiya a hanyar Kaduna zuwa Abuja wani tashin hankali ne. Sokoto, Katsina da sauran jihohinmu na arewa ba mu da nutsuwa, wanda gwamnati tana gani ta san halin da ake ciki. Kuma duk Jami’an tsaron nan manya-manyansu ‘yan Arewa ne, hatta shi kansa shugaban kasa dan arewa ne amma duk matsalolin nan a kan arewa ya tsaya.”

Galadanci ya ce, matsalolin tsaro sun haifar da talauci da yunwa a tsakanin jama’a, “Mafita shi ne ‘yan arewa su tsaya su kwaci ‘yancin kansu. PDP ta yi Mulki mun gani, APC ta yi mun gani, yanzu ‘yan Nijeriya su ne za su yi wa kansu zabi wanda za su samu mafita a wannan lokacin.”

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Ya ce tabbas Nijeriya babu shugabanni nagari, “abun kunya yara da suke karatu a jami’o’i yau watansu nawa a gida? Ba wanda ya fito ya yi magana domin ‘ya’yan shugabannin ba a Nijeriya suke karatu ba.”

“Kullum fa dan arewa shine aka bari cikin damuwa, ka bar Arewa ka zo sana’a a Kudu ma a kama ka a kai ka kurkuku ba ka yi laifi ba, ba wani abu ba wanda zai bi kadin ka. Muna zaune ne kawai zaman dole ba yadda za mu yi.” In ji shi.

  • https://en.m.wikipedia.org/wiki/Arewa

Ya yi kira ga ‘yan arewa su tabbatar da shugabanni nagari kadai ne suka zaba a 2023 domin fita daga wannan kangi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Brazil Ta Ci Gaba Da Zama Ta Daya A Duniya

Next Post

Darussa Daga Aikin Hajjin Manzon Allah (SAW)

Related

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025
Labarai

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

3 hours ago
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna
Labarai

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

3 hours ago
Tinubu
Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

4 hours ago
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano
Labarai

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

5 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake ÆŠage Ranar Komawa Makarantu
Labarai

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

6 hours ago
Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

8 hours ago
Next Post
Abubuwan Da Aka Halatta Da Wadanda Aka Haramta Ga Mahajjaci (II)

Darussa Daga Aikin Hajjin Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

Rundunar NSCDC Ta Kama Wani Da Ake Zargi Da Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kano

August 6, 2025
Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

Kasar Sin Za Ta Nuna Goyon Baya Ga Sabbin Masana’antu Ta Hanyar Hada-Hadar Kudi

August 6, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake ÆŠage Ranar Komawa Makarantu

“Ku Yi Murabus Idan Baza Ku Iya Rike Amanar Jama’a ba” – Gargadin Gwamna Abba Ga Kwamishinoninsa

August 6, 2025
Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

Sin Ya Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Aiwatar Da Mataki Mai Hadari A Zirin Gaza

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.