• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Shugabanni Na Kwarai Ke Kara Rura Matsalolin Arewa – Ibrahim Galadanci

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Rashin Shugabanni Na Kwarai Ke Kara Rura Matsalolin Arewa – Ibrahim Galadanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Gamayyar Kungiyoyin Matasan Arewa mazauna Jihar Legas, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci, ya bayyana cewar, rashin shugabanni na kwarai da ake fama da shi a Nijeriya na daga cikin manyan matsalolin da suke janyo koma baya ga Arewa.

Ya ce, hatta matsalolin tsaron da ake ta fama da su, rashin adilan shugabanni ne ke kara janyo matsalar, sai ya bukaci ‘yan Nijeriya musamman ‘yan Arewa da su yi amfani da lokacin zaben 2023 wajen zaban Shugabanni na kwarai da za su iya kyautata rayuwar al’umma.

  • Buhari Ya Jinjina Wa Portugal Kan Samar Da Tsaro A Afrika

“Wannan matsalar sakacin shugabanni ne domin ba mu da Shugabanni wadanda suke kokarin kare ‘yancin ‘yan Arewa ma baki daya, domin da muna da su da wadannan abubuwan ba za su ci gaba da faruwa ba don iyaka yankin arewa ake wannan abun.

“Dan arewa ba shi da ‘yancin zuwa gona ko kasuwa ko hawa hanya, yanzu ka duba tafiya a hanyar Kaduna zuwa Abuja wani tashin hankali ne. Sokoto, Katsina da sauran jihohinmu na arewa ba mu da nutsuwa, wanda gwamnati tana gani ta san halin da ake ciki. Kuma duk Jami’an tsaron nan manya-manyansu ‘yan Arewa ne, hatta shi kansa shugaban kasa dan arewa ne amma duk matsalolin nan a kan arewa ya tsaya.”

Galadanci ya ce, matsalolin tsaro sun haifar da talauci da yunwa a tsakanin jama’a, “Mafita shi ne ‘yan arewa su tsaya su kwaci ‘yancin kansu. PDP ta yi Mulki mun gani, APC ta yi mun gani, yanzu ‘yan Nijeriya su ne za su yi wa kansu zabi wanda za su samu mafita a wannan lokacin.”

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

Ya ce tabbas Nijeriya babu shugabanni nagari, “abun kunya yara da suke karatu a jami’o’i yau watansu nawa a gida? Ba wanda ya fito ya yi magana domin ‘ya’yan shugabannin ba a Nijeriya suke karatu ba.”

“Kullum fa dan arewa shine aka bari cikin damuwa, ka bar Arewa ka zo sana’a a Kudu ma a kama ka a kai ka kurkuku ba ka yi laifi ba, ba wani abu ba wanda zai bi kadin ka. Muna zaune ne kawai zaman dole ba yadda za mu yi.” In ji shi.

  • https://en.m.wikipedia.org/wiki/Arewa

Ya yi kira ga ‘yan arewa su tabbatar da shugabanni nagari kadai ne suka zaba a 2023 domin fita daga wannan kangi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Brazil Ta Ci Gaba Da Zama Ta Daya A Duniya

Next Post

Darussa Daga Aikin Hajjin Manzon Allah (SAW)

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

12 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

13 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

14 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

15 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

17 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

17 hours ago
Next Post
Abubuwan Da Aka Halatta Da Wadanda Aka Haramta Ga Mahajjaci (II)

Darussa Daga Aikin Hajjin Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.