ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Shugabanni Na Kwarai Ke Kara Rura Matsalolin Arewa – Ibrahim Galadanci

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Shugabanni

Shugaban Gamayyar Kungiyoyin Matasan Arewa mazauna Jihar Legas, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci, ya bayyana cewar, rashin shugabanni na kwarai da ake fama da shi a Nijeriya na daga cikin manyan matsalolin da suke janyo koma baya ga Arewa.

Ya ce, hatta matsalolin tsaron da ake ta fama da su, rashin adilan shugabanni ne ke kara janyo matsalar, sai ya bukaci ‘yan Nijeriya musamman ‘yan Arewa da su yi amfani da lokacin zaben 2023 wajen zaban Shugabanni na kwarai da za su iya kyautata rayuwar al’umma.

  • Buhari Ya Jinjina Wa Portugal Kan Samar Da Tsaro A Afrika

“Wannan matsalar sakacin shugabanni ne domin ba mu da Shugabanni wadanda suke kokarin kare ‘yancin ‘yan Arewa ma baki daya, domin da muna da su da wadannan abubuwan ba za su ci gaba da faruwa ba don iyaka yankin arewa ake wannan abun.

ADVERTISEMENT

“Dan arewa ba shi da ‘yancin zuwa gona ko kasuwa ko hawa hanya, yanzu ka duba tafiya a hanyar Kaduna zuwa Abuja wani tashin hankali ne. Sokoto, Katsina da sauran jihohinmu na arewa ba mu da nutsuwa, wanda gwamnati tana gani ta san halin da ake ciki. Kuma duk Jami’an tsaron nan manya-manyansu ‘yan Arewa ne, hatta shi kansa shugaban kasa dan arewa ne amma duk matsalolin nan a kan arewa ya tsaya.”

Galadanci ya ce, matsalolin tsaro sun haifar da talauci da yunwa a tsakanin jama’a, “Mafita shi ne ‘yan arewa su tsaya su kwaci ‘yancin kansu. PDP ta yi Mulki mun gani, APC ta yi mun gani, yanzu ‘yan Nijeriya su ne za su yi wa kansu zabi wanda za su samu mafita a wannan lokacin.”

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Ya ce tabbas Nijeriya babu shugabanni nagari, “abun kunya yara da suke karatu a jami’o’i yau watansu nawa a gida? Ba wanda ya fito ya yi magana domin ‘ya’yan shugabannin ba a Nijeriya suke karatu ba.”

“Kullum fa dan arewa shine aka bari cikin damuwa, ka bar Arewa ka zo sana’a a Kudu ma a kama ka a kai ka kurkuku ba ka yi laifi ba, ba wani abu ba wanda zai bi kadin ka. Muna zaune ne kawai zaman dole ba yadda za mu yi.” In ji shi.

  • https://en.m.wikipedia.org/wiki/Arewa

Ya yi kira ga ‘yan arewa su tabbatar da shugabanni nagari kadai ne suka zaba a 2023 domin fita daga wannan kangi.

Shugabanni
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
Labarai

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Next Post
Abubuwan Da Aka Halatta Da Wadanda Aka Haramta Ga Mahajjaci (II)

Darussa Daga Aikin Hajjin Manzon Allah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.