• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rasuwar Buhari: An Yi Rashin Ɗan Ƙasa Na Gari, Abin Koyi — Kungiyar Gwamnonin Arewa

by Abba Ibrahim Wada and Muhammad
3 months ago
Buhari

Kungiyar Gwamnonin Arewacin Nijeriya ta bayyana alhininta kan rasuwar tsohon shugaban ƙasa, Muhammad Buhari, inda ta bayyana rasuwarsa a matsayin babban rashi a ƙasa baki ɗaya.

A cikin saƙon ta’aziyya da ƙungiyar ta fitar mai ɗauke da sa hannun shugaban ƙungiyar kuma gwamnan jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya, gwamnonin sun yabawa shugaban wajen jajircewa da gaskiya da kuma hidimtawa ƙasa.

  • Tinubu Ya Tabbatar da Rasuwar Buhari, Ya Tura Shettima Zuwa Landan
  • Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

“Shugaba Muhammad Buhari babban mutum ne wanda ya yi riƙo da gaskiya da amana da kuma hidimtawa al’ummar Nijeriya” A cewar ƙungiyar gwamnonin.

Kungiyar ta ci gaba da cewa “Tun daga rayuwarsa a matsayin matashin soja da lokacin da ya zama shugaban ƙasa na mulkin soja da na farar hula, Buhari ya kasance mutum mai mutunci da sanin ya kamata. Za a dinga tuna shi wajen sadaukar da kai da rashin son kansa da kuma mayar da hankali wajen aiki ga al’umma da haɗin kan ƙasa da samar da tsaro da ci gaban ƙasarmu”

Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana Buhari a matsayin abin koyi musamman ga ƙungiyar gwamnonin Arewa, inda ya bayyana irin tsarin da marigayin yake da shi na gaskiya da yin gwamnati a buɗe.

LABARAI MASU NASABA

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

“A wajenmu ƙungiyar gwamnonin Arewa, Buhari ba iya kawai babban mutum bane a ƙasa, abin koyi ne wanda a ko koyaushe yake tsayawa a kan gaskiya da adalci da kuma riƙon amana. Ya koyar da mutane cikin mutunci , ya yi mulki da ƙwarin gwiwa sannan ya rayu, rayuwa mai sauƙi” in ji gwamnan na Gombe.

Inuwa Yahaya ya ce rasuwar Buhari ta bar gagarumin giɓi wanda kuma za a jima ana jimami.

Tsohon shugaban dai ya rasu ne a yammacin ranar Lahadi a birnin London yana da shekara 82 a duniya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba
Labarai

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Next Post
Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari Ya Rasu A Landan

Rasuwar Buhari: Nahiyar Afirka Ta Yi Babban Rashi — Kungiyar Gwamnoni Ta Nijeriya 

LABARAI MASU NASABA

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.