ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

by Muhammad
11 months ago
Buhari

An haifi Muhammadu Buhari a ranar 17, ga Disamba, 1942, a garin Daura na Jihar Katsina, Nijeriya. Shi ne ɗa na 23 a cikin yaran Malam Harɗo Adamu, wani shugaba Fulani da ya fito daga garin Dumurkul da ke ƙaramar hukumar Mai’Adua ta jihar Katsina, da mahaifiyarsa Zulaihat. 

Tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari shi ne mutum na shida da aka zaɓa ta hanyar dimokuraɗiyya a Nijeriya, Muhammadu Buhari, ya rasu yana da shekaru 82 (2025 – 1942) a yammacin a ranar Lahadi a wani asibiti da ke birnin Landan bayan ya sha fama da doguwar rashin lafiya.

  • Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari Ya Rasu A Landan
  • Tinubu Ya Tabbatar da Rasuwar Buhari, Ya Tura Shettima Zuwa Landan

Ga wasu manyan abubuwa 10 da kowa zai so ya sani game da rayuwar Marigayi Buhari:

ADVERTISEMENT

1. Hawa Shugabanci Karo Biyu – Soja Da Siyasa
Buhari ya shugabanci Nijeriya a matsayin shugaban mulkin soja daga 1983 zuwa 1985, sannan kuma aka zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa a 2015 zuwa 2023.

2. Ƙwararren Soja, Ɗan Yaƙin Basasa
Ya shiga soja a 1962, ya samu horo a Burtaniya, kuma ya yi yaki a lokacin yaƙin basasa, inda ya jagoranci bataliya da manyan hare-hare a yankin gabas.

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

3. Ƙaddamar Da Yaƙi Da Rashin Ɗa’a (WAI)
A mulkinsa na soja, Buhari ya ƙaddamar da shahararren shirin yaƙi da rashin ɗa’a, don ya gyara halayen jama’a da ƙarfafa kyawawan ɗabi’u da kishin ƙasa.

4. Mulki Tsauri A Shekarun 1980
Mulkinsa na soja ya ƙunshi dokoki masu tsauri da daure ’yan jarida da sallamar ma’aikata daj yanke hukuncin kisa ga masu safarar miyagun ƙwayoyi.

5. Shugabantar Kula Da Asusun PTF
A ƙarƙashin mulkin Janar Abacha, Buhari ya shugabanci PTF, inda aka yabawa ayyukansa na1 gaskiya da gina ababen more rayuwa.

6. Ya Yi Takara Huɗu, Ya Ci Zaɓe A Karo Na Ƙarshe
Buhari ya tsaya takara a 2003 da 2007 da 2011, amma sai a shekarar 2015 ya lashe zaɓe a matsayin shugaban ƙasa kuma ɗan jam’iyyar APC, inda ya kayar da Shugaba Goodluck Jonathan.

7. Ya Mayar Da Hankali Kan Yaƙi Da Rashawa Da Samar Da Tsaro
A mulkinsa na farar hula, ya mayar da hankali kan yaƙi da rashawa da yaƙi da Boko Haram da samar da shirye-shiryen tallafawa matasa kamar shirin N-Power.

8. Doguwar Jinya Ta Yi Tasiri A Mulkinsa
Ya sha barin ƙasa don neman lafiya, ciki har da watanni huɗu a 2017, lamarin da ya jawo damuwa da firgici kan yanayin lafiyarsa da tafiyar da mulki.

9. Ƙalubalen Zanga-Zangar #EndSARS
A 2020, gwamnatinsa ta fuskanci babbar zanga-zangar matasa kan cin zarafin ’yansanda (#EndSARS), wadda ta zama jigo a tarihin mulkinsa.

10. Miƙa Mulki Cikin Lumana Da Komawa Daura
A ranar 29 ga Mayu, 2023, ya miƙa mulki ga Shugaba Tinubu, sannan ya koma mahaifarsa garin Daura na jihar Katsina, bayan ya kammala aikin gwamnati na aƙaalla shekaru 50.

Buhari
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Rahotonni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
Rahotonni

Matsalar Tsaro:Kashi 60 Na Masana’antu A Arewa Maso Gabas Sun Durƙushe

June 19, 2026
Next Post
Afirka Ta Kudu Na Fatan Karfafa Alakar Cinikayya Tare Da Sin Ta Hanyar Halartar Baje Kolin CISCE

Afirka Ta Kudu Na Fatan Karfafa Alakar Cinikayya Tare Da Sin Ta Hanyar Halartar Baje Kolin CISCE

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.