ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Raya Kasa Bisa Yanayin Da Kasar Ke Ciki

by CMG Hausa
3 years ago
Raya kasa

Kwanakin baya, na ziyarci wani lambun ‘ya’yan itatuwa dake yankin karkarar birnin Beijing na kasar Sin, inda ake yin amfani da na’urorin zamani har nau’ika 28, wajen gudanar da aikin gona.

A baya ana bukatar ma’aikata masu kula da lambun har 60, amma yanzu mutane 6 ne kacal ake bukata, inda suke sarrafa injuna masu gudanar da dukkan ayyuka daban daban.

  • Kasar Sin Za Ta Kara Bude Kofarta Ga Kasashen Ketare

Shin yawan yin amfani da injuna zai sa manoma su rasa guraben aikin yi? A’a, ba haka ba ne. Wani farfesa mai suna He Xiongkui dake samar da fasahohin zamani ga wannan lambun ‘ya’yan itatuwa ya gaya mana cewa, yanzu haka ci gaban biranen kasar Sin ya sa matasan kauyukan kasar kaura zuwa cikin birane, don neman zaman rayuwa mafi inganci, lamarin da ya haddasa karancin ma’aikata a yankunan karkara.

ADVERTISEMENT

Don daidaita wannan matsala, dole ne a kara yin amfani da na’urorin zamani wajen gudanar da aikin gona. Wannan dabara ce da kasar Sin ta dauka, a kokarin zamanintar da aikin gona, kana ta nuna wata halayyar musamman ta dabarar raya kasa ta kasar Sin, wato “zabar hanyar da ta dace da yanayin da kasar ke ciki”.

Wannan halayya ta sa hanyar da kasar Sin ke bi a kokarin zamanintar da kai ta sha bamban da ta kasashen yamma, hakan na nuna cewa Sin ba za ta yi koyi da dabarun wasu kasashe na yakar sauran kasashe ba, da yin mulkin mallaka, da kwatar dukiyoyin al’ummun duniya.

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

A maimakon haka, kasar Sin na tsayawa kan hanyar raya kasa cikin lumana. Idan mun nazarci tarihin Sin, za mu ga cewa, tsakanin shekarar 1840 da ta 1945, bi da bi ne wasu kasashen Turai da ma kasar Japan, suka kai wutar yaki kasar Sin daya bayan daya, lamarin da ya jefa kasar Sin cikin yanayi mai matukar wuya. Kana kasar ta dade ba ta samu farfadowa ba, kafin ta zama cikin wani yanayi na zaman lafiya a shekaru gomai da suka wuce.

Kamar yadda Hausawa kan ce “Kowa ya san ciwon kansa, ya san na wani”. Wannan tarihi na fama da hare-haren da wasu kasashen waje suka kai mata, ya sa kasar Sin zama wata kasar dake iyakacin kokarin tabbatar da zaman lafiya a duniya.

Ban da wannan kuma, tunanin “zabar hanyar raya kasa mai dacewa da yanayin da kasar ke ciki” shi ma ya sa kasar Sin saka buri na baiwa dukkan al’ummun kasar damar samun wadata.

Dalilin da ya sa haka, shi ne tsarin siyasa na Gurguzu na kasar. Wannan tsarin ya sa ana kokarin tabbatar da adalci a zaman al’ummar kasar, da magance karuwar gibi tsakanin al’umma.

Hakika a cikin shekaru fiye da 40 da suka wuce, hukumar kasar Sin ta fid da kimanin mutane miliyan 800 daga kangin talauci. Wannan jimilla ta shaida kokarin gwamnatin kasar na neman wadatar da dukkan al’ummun ta.

Haka zalika, yadda ake raya kasa bisa yanayin da kasar ke ciki shi ma ya sa kasancewar al’ummar kasar karkashin jagorancin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta zama dole.

Idan mun waiwayi baya, za mu ga yadda a cikin shekaru fiye da 100 da suka wuce, jam’iyyar ta yi kokarin daidaita matsalolin da kasar ke fuskanta, gami da yi wa kanta kwaskwarima, ta yadda sannu a hankali, kasar ta raya kanta, daga wata kasa mai raunin tattalin arziki, zuwa wata kasar da karfin tattalin arzikinta ya zama na biyu a duniya.

Ta hanyar gudanar da mulki cikin nasara, jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ta shaida kwarewarta a fannin yin gyare-gyare, da tsara shiri na dogon lokaci, tare da samun cikakken goyon baya daga jama’ar kasar.
Yadda kasar Sin take la’akari da yanayin kanta, ya sa ta zabar dabarar raya kasa da ta sha bamban da ta kasashen yamma.

Kamar dai yadda Hausawa su kan ce, “Kayan aro ba ya rufe katara”, kana “Ko wace kwarya tana da marufinta”, abun da ya fi muhimmanci, shi ne zabar turba mai dacewa da kai, wadda za ta haifar da hakikanin ci gaban kasa. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow
Daga Birnin Sin

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
NDLEA Ta Cafke Wani Basaraken Kauye Da Wasu Kan Safarar Miyagun Kwayoyi

NDLEA Na Neman Wani Dillalin Kwayoyi Ruwa A Jallo A Jihar Legas

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.