• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Raya Kasa Bisa Yanayin Da Kasar Ke Ciki

byCMG Hausa
3 years ago
Raya kasa

Kwanakin baya, na ziyarci wani lambun ‘ya’yan itatuwa dake yankin karkarar birnin Beijing na kasar Sin, inda ake yin amfani da na’urorin zamani har nau’ika 28, wajen gudanar da aikin gona.

A baya ana bukatar ma’aikata masu kula da lambun har 60, amma yanzu mutane 6 ne kacal ake bukata, inda suke sarrafa injuna masu gudanar da dukkan ayyuka daban daban.

  • Kasar Sin Za Ta Kara Bude Kofarta Ga Kasashen Ketare

Shin yawan yin amfani da injuna zai sa manoma su rasa guraben aikin yi? A’a, ba haka ba ne. Wani farfesa mai suna He Xiongkui dake samar da fasahohin zamani ga wannan lambun ‘ya’yan itatuwa ya gaya mana cewa, yanzu haka ci gaban biranen kasar Sin ya sa matasan kauyukan kasar kaura zuwa cikin birane, don neman zaman rayuwa mafi inganci, lamarin da ya haddasa karancin ma’aikata a yankunan karkara.

Don daidaita wannan matsala, dole ne a kara yin amfani da na’urorin zamani wajen gudanar da aikin gona. Wannan dabara ce da kasar Sin ta dauka, a kokarin zamanintar da aikin gona, kana ta nuna wata halayyar musamman ta dabarar raya kasa ta kasar Sin, wato “zabar hanyar da ta dace da yanayin da kasar ke ciki”.

Wannan halayya ta sa hanyar da kasar Sin ke bi a kokarin zamanintar da kai ta sha bamban da ta kasashen yamma, hakan na nuna cewa Sin ba za ta yi koyi da dabarun wasu kasashe na yakar sauran kasashe ba, da yin mulkin mallaka, da kwatar dukiyoyin al’ummun duniya.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

A maimakon haka, kasar Sin na tsayawa kan hanyar raya kasa cikin lumana. Idan mun nazarci tarihin Sin, za mu ga cewa, tsakanin shekarar 1840 da ta 1945, bi da bi ne wasu kasashen Turai da ma kasar Japan, suka kai wutar yaki kasar Sin daya bayan daya, lamarin da ya jefa kasar Sin cikin yanayi mai matukar wuya. Kana kasar ta dade ba ta samu farfadowa ba, kafin ta zama cikin wani yanayi na zaman lafiya a shekaru gomai da suka wuce.

Kamar yadda Hausawa kan ce “Kowa ya san ciwon kansa, ya san na wani”. Wannan tarihi na fama da hare-haren da wasu kasashen waje suka kai mata, ya sa kasar Sin zama wata kasar dake iyakacin kokarin tabbatar da zaman lafiya a duniya.

Ban da wannan kuma, tunanin “zabar hanyar raya kasa mai dacewa da yanayin da kasar ke ciki” shi ma ya sa kasar Sin saka buri na baiwa dukkan al’ummun kasar damar samun wadata.

Dalilin da ya sa haka, shi ne tsarin siyasa na Gurguzu na kasar. Wannan tsarin ya sa ana kokarin tabbatar da adalci a zaman al’ummar kasar, da magance karuwar gibi tsakanin al’umma.

Hakika a cikin shekaru fiye da 40 da suka wuce, hukumar kasar Sin ta fid da kimanin mutane miliyan 800 daga kangin talauci. Wannan jimilla ta shaida kokarin gwamnatin kasar na neman wadatar da dukkan al’ummun ta.

Haka zalika, yadda ake raya kasa bisa yanayin da kasar ke ciki shi ma ya sa kasancewar al’ummar kasar karkashin jagorancin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta zama dole.

Idan mun waiwayi baya, za mu ga yadda a cikin shekaru fiye da 100 da suka wuce, jam’iyyar ta yi kokarin daidaita matsalolin da kasar ke fuskanta, gami da yi wa kanta kwaskwarima, ta yadda sannu a hankali, kasar ta raya kanta, daga wata kasa mai raunin tattalin arziki, zuwa wata kasar da karfin tattalin arzikinta ya zama na biyu a duniya.

Ta hanyar gudanar da mulki cikin nasara, jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ta shaida kwarewarta a fannin yin gyare-gyare, da tsara shiri na dogon lokaci, tare da samun cikakken goyon baya daga jama’ar kasar.
Yadda kasar Sin take la’akari da yanayin kanta, ya sa ta zabar dabarar raya kasa da ta sha bamban da ta kasashen yamma.

Kamar dai yadda Hausawa su kan ce, “Kayan aro ba ya rufe katara”, kana “Ko wace kwarya tana da marufinta”, abun da ya fi muhimmanci, shi ne zabar turba mai dacewa da kai, wadda za ta haifar da hakikanin ci gaban kasa. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
NDLEA Ta Cafke Wani Basaraken Kauye Da Wasu Kan Safarar Miyagun Kwayoyi

NDLEA Na Neman Wani Dillalin Kwayoyi Ruwa A Jallo A Jihar Legas

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version