• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Raya Kasa Bisa Yanayin Da Kasar Ke Ciki

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Raya Kasa Bisa Yanayin Da Kasar Ke Ciki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanakin baya, na ziyarci wani lambun ‘ya’yan itatuwa dake yankin karkarar birnin Beijing na kasar Sin, inda ake yin amfani da na’urorin zamani har nau’ika 28, wajen gudanar da aikin gona.

A baya ana bukatar ma’aikata masu kula da lambun har 60, amma yanzu mutane 6 ne kacal ake bukata, inda suke sarrafa injuna masu gudanar da dukkan ayyuka daban daban.

  • Kasar Sin Za Ta Kara Bude Kofarta Ga Kasashen Ketare

Shin yawan yin amfani da injuna zai sa manoma su rasa guraben aikin yi? A’a, ba haka ba ne. Wani farfesa mai suna He Xiongkui dake samar da fasahohin zamani ga wannan lambun ‘ya’yan itatuwa ya gaya mana cewa, yanzu haka ci gaban biranen kasar Sin ya sa matasan kauyukan kasar kaura zuwa cikin birane, don neman zaman rayuwa mafi inganci, lamarin da ya haddasa karancin ma’aikata a yankunan karkara.

Don daidaita wannan matsala, dole ne a kara yin amfani da na’urorin zamani wajen gudanar da aikin gona. Wannan dabara ce da kasar Sin ta dauka, a kokarin zamanintar da aikin gona, kana ta nuna wata halayyar musamman ta dabarar raya kasa ta kasar Sin, wato “zabar hanyar da ta dace da yanayin da kasar ke ciki”.

Wannan halayya ta sa hanyar da kasar Sin ke bi a kokarin zamanintar da kai ta sha bamban da ta kasashen yamma, hakan na nuna cewa Sin ba za ta yi koyi da dabarun wasu kasashe na yakar sauran kasashe ba, da yin mulkin mallaka, da kwatar dukiyoyin al’ummun duniya.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

A maimakon haka, kasar Sin na tsayawa kan hanyar raya kasa cikin lumana. Idan mun nazarci tarihin Sin, za mu ga cewa, tsakanin shekarar 1840 da ta 1945, bi da bi ne wasu kasashen Turai da ma kasar Japan, suka kai wutar yaki kasar Sin daya bayan daya, lamarin da ya jefa kasar Sin cikin yanayi mai matukar wuya. Kana kasar ta dade ba ta samu farfadowa ba, kafin ta zama cikin wani yanayi na zaman lafiya a shekaru gomai da suka wuce.

Kamar yadda Hausawa kan ce “Kowa ya san ciwon kansa, ya san na wani”. Wannan tarihi na fama da hare-haren da wasu kasashen waje suka kai mata, ya sa kasar Sin zama wata kasar dake iyakacin kokarin tabbatar da zaman lafiya a duniya.

Ban da wannan kuma, tunanin “zabar hanyar raya kasa mai dacewa da yanayin da kasar ke ciki” shi ma ya sa kasar Sin saka buri na baiwa dukkan al’ummun kasar damar samun wadata.

Dalilin da ya sa haka, shi ne tsarin siyasa na Gurguzu na kasar. Wannan tsarin ya sa ana kokarin tabbatar da adalci a zaman al’ummar kasar, da magance karuwar gibi tsakanin al’umma.

Hakika a cikin shekaru fiye da 40 da suka wuce, hukumar kasar Sin ta fid da kimanin mutane miliyan 800 daga kangin talauci. Wannan jimilla ta shaida kokarin gwamnatin kasar na neman wadatar da dukkan al’ummun ta.

Haka zalika, yadda ake raya kasa bisa yanayin da kasar ke ciki shi ma ya sa kasancewar al’ummar kasar karkashin jagorancin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta zama dole.

Idan mun waiwayi baya, za mu ga yadda a cikin shekaru fiye da 100 da suka wuce, jam’iyyar ta yi kokarin daidaita matsalolin da kasar ke fuskanta, gami da yi wa kanta kwaskwarima, ta yadda sannu a hankali, kasar ta raya kanta, daga wata kasa mai raunin tattalin arziki, zuwa wata kasar da karfin tattalin arzikinta ya zama na biyu a duniya.

Ta hanyar gudanar da mulki cikin nasara, jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ta shaida kwarewarta a fannin yin gyare-gyare, da tsara shiri na dogon lokaci, tare da samun cikakken goyon baya daga jama’ar kasar.
Yadda kasar Sin take la’akari da yanayin kanta, ya sa ta zabar dabarar raya kasa da ta sha bamban da ta kasashen yamma.

Kamar dai yadda Hausawa su kan ce, “Kayan aro ba ya rufe katara”, kana “Ko wace kwarya tana da marufinta”, abun da ya fi muhimmanci, shi ne zabar turba mai dacewa da kai, wadda za ta haifar da hakikanin ci gaban kasa. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Cafke Wani Dan Siyasa Da Wasu Kan Satar Kudin Banki N1.4bn A Jihar Kogi

Next Post

NDLEA Na Neman Wani Dillalin Kwayoyi Ruwa A Jallo A Jihar Legas

Related

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

7 hours ago
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?
Daga Birnin Sin

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

8 hours ago
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe
Daga Birnin Sin

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

9 hours ago
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

10 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 

11 hours ago
Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu

12 hours ago
Next Post
NDLEA Ta Cafke Wani Basaraken Kauye Da Wasu Kan Safarar Miyagun Kwayoyi

NDLEA Na Neman Wani Dillalin Kwayoyi Ruwa A Jallo A Jihar Legas

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.