ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Raya Kasa Bisa Yanayin Da Kasar Ke Ciki

by CMG Hausa
4 years ago
Raya kasa

Kwanakin baya, na ziyarci wani lambun ‘ya’yan itatuwa dake yankin karkarar birnin Beijing na kasar Sin, inda ake yin amfani da na’urorin zamani har nau’ika 28, wajen gudanar da aikin gona.

A baya ana bukatar ma’aikata masu kula da lambun har 60, amma yanzu mutane 6 ne kacal ake bukata, inda suke sarrafa injuna masu gudanar da dukkan ayyuka daban daban.

  • Kasar Sin Za Ta Kara Bude Kofarta Ga Kasashen Ketare

Shin yawan yin amfani da injuna zai sa manoma su rasa guraben aikin yi? A’a, ba haka ba ne. Wani farfesa mai suna He Xiongkui dake samar da fasahohin zamani ga wannan lambun ‘ya’yan itatuwa ya gaya mana cewa, yanzu haka ci gaban biranen kasar Sin ya sa matasan kauyukan kasar kaura zuwa cikin birane, don neman zaman rayuwa mafi inganci, lamarin da ya haddasa karancin ma’aikata a yankunan karkara.

ADVERTISEMENT

Don daidaita wannan matsala, dole ne a kara yin amfani da na’urorin zamani wajen gudanar da aikin gona. Wannan dabara ce da kasar Sin ta dauka, a kokarin zamanintar da aikin gona, kana ta nuna wata halayyar musamman ta dabarar raya kasa ta kasar Sin, wato “zabar hanyar da ta dace da yanayin da kasar ke ciki”.

Wannan halayya ta sa hanyar da kasar Sin ke bi a kokarin zamanintar da kai ta sha bamban da ta kasashen yamma, hakan na nuna cewa Sin ba za ta yi koyi da dabarun wasu kasashe na yakar sauran kasashe ba, da yin mulkin mallaka, da kwatar dukiyoyin al’ummun duniya.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

A maimakon haka, kasar Sin na tsayawa kan hanyar raya kasa cikin lumana. Idan mun nazarci tarihin Sin, za mu ga cewa, tsakanin shekarar 1840 da ta 1945, bi da bi ne wasu kasashen Turai da ma kasar Japan, suka kai wutar yaki kasar Sin daya bayan daya, lamarin da ya jefa kasar Sin cikin yanayi mai matukar wuya. Kana kasar ta dade ba ta samu farfadowa ba, kafin ta zama cikin wani yanayi na zaman lafiya a shekaru gomai da suka wuce.

Kamar yadda Hausawa kan ce “Kowa ya san ciwon kansa, ya san na wani”. Wannan tarihi na fama da hare-haren da wasu kasashen waje suka kai mata, ya sa kasar Sin zama wata kasar dake iyakacin kokarin tabbatar da zaman lafiya a duniya.

Ban da wannan kuma, tunanin “zabar hanyar raya kasa mai dacewa da yanayin da kasar ke ciki” shi ma ya sa kasar Sin saka buri na baiwa dukkan al’ummun kasar damar samun wadata.

Dalilin da ya sa haka, shi ne tsarin siyasa na Gurguzu na kasar. Wannan tsarin ya sa ana kokarin tabbatar da adalci a zaman al’ummar kasar, da magance karuwar gibi tsakanin al’umma.

Hakika a cikin shekaru fiye da 40 da suka wuce, hukumar kasar Sin ta fid da kimanin mutane miliyan 800 daga kangin talauci. Wannan jimilla ta shaida kokarin gwamnatin kasar na neman wadatar da dukkan al’ummun ta.

Haka zalika, yadda ake raya kasa bisa yanayin da kasar ke ciki shi ma ya sa kasancewar al’ummar kasar karkashin jagorancin jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta zama dole.

Idan mun waiwayi baya, za mu ga yadda a cikin shekaru fiye da 100 da suka wuce, jam’iyyar ta yi kokarin daidaita matsalolin da kasar ke fuskanta, gami da yi wa kanta kwaskwarima, ta yadda sannu a hankali, kasar ta raya kanta, daga wata kasa mai raunin tattalin arziki, zuwa wata kasar da karfin tattalin arzikinta ya zama na biyu a duniya.

Ta hanyar gudanar da mulki cikin nasara, jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, ta shaida kwarewarta a fannin yin gyare-gyare, da tsara shiri na dogon lokaci, tare da samun cikakken goyon baya daga jama’ar kasar.
Yadda kasar Sin take la’akari da yanayin kanta, ya sa ta zabar dabarar raya kasa da ta sha bamban da ta kasashen yamma.

Kamar dai yadda Hausawa su kan ce, “Kayan aro ba ya rufe katara”, kana “Ko wace kwarya tana da marufinta”, abun da ya fi muhimmanci, shi ne zabar turba mai dacewa da kai, wadda za ta haifar da hakikanin ci gaban kasa. (Bello Wang)

Raya kasa
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
NDLEA Ta Cafke Wani Basaraken Kauye Da Wasu Kan Safarar Miyagun Kwayoyi

NDLEA Na Neman Wani Dillalin Kwayoyi Ruwa A Jallo A Jihar Legas

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.