Barista Hudu Yunusa Ari, kwamishinan hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a jihar Adamawa, yayi zargin cewa, rayuwarsa na cikin hadari.
Hudu Ari, ya bayyana haka lokacin da yake ganawa da manema labarai a gidansa dake Bauchi, ya kuma bada tabbacin duk da rayuwarsa na cikin hadari, INEC zata gudanar da karbabben zabe bisa gaskiya da adalci.
Ya ci gaba da cewa “amatsayina na kwamishinan hukumar zabe INEC bana tare da kowace jam’iyya, ko dantakara, dukkansu daya suke a wajena, bani da wani dalilin kin wani ko goyon bayan wani dantakara ko jam’iyya” inji Ari.
Haka kuma shugaban hukumar zaben yayi Allawadai da barazanar da’ake yiwa lafiyarsa yace “mun waye gari a bariki, abin bakin ciki haka ke faruwa, jami’an sokoji suka kubutar damu” inji shi.
Da yake magana game da batun sake kidaya sakamakon zaben kuwa Hudu Yunusa Ari, yace hukumar INEC ta kasa ke da ta cewa akai, “Ni a shirye na ke na aiwatar da duk umurnin da hedikwatar INEC ta bani” ya jaddada.
To sai dai, wani sakon murya ta bayyana lokacin zaben kujerar gwamnan, da kwamishinan hukumar zaben Hudu Yunusa Ari, ke bada umurnin ataimaki matannan ta lashe zabe, lamarin da ya haifar da ce-ce ko-ce.
Yanzu INEC ta sanar da ranar 15 ga Afrilun 2023, ranar da hukumar zaben za ta sake zabe a wasu cibiyoyin kada kuri’a 69 a jihar, da zai baiwa hukumar damar sanar da jam’iyyar da ta lashe zaben kujerar gwamna a jihar
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp