• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rayuwar Amina Muhammad, Mataimakiyar Sakatare-Janar Na Majalisar Dinkin Duniya A Takaice

by Bushira Nakura
2 years ago
in Adon Gari
0
Rayuwar Amina Muhammad, Mataimakiyar Sakatare-Janar Na Majalisar Dinkin Duniya A Takaice

As a prelude to the celebration of International Women's Day, the Central African Minister of Social Action and Family, Ms. Gisel PANA, visited the women in Bimbo Women's Prison and Corrections. On occasion, women prisoners have exhibited for sale works produced as part of Income Generating Activities, with the support of MINUSCA. An action aimed at contributing to their reintegration.www.icj-cij.org

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Madam Amina J. Mohammed ita ce mataimakiyar Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya kuma shugabar kungiyar ci gaba mai dorewa ta Majalisar Dinkin Duniya.

Idan za a tunawa Amina Mohammed ta rike Minista a gwamnatin Muhammadu Buhari kafin ta zama mataimakiyar sakatariyar majalisar UN a 2017.

  • Yadda Likita Ya Yi Lalata Da Wata Mai Jinya A Asibitinsa A Jihar Kwara
  • Manyan Jami’an Kasashen Sin Da Amurka Sun Tattauna Game Da Alakar Kasashen Biyu

Kafin nadin nata, Ms. Mohammed ta kasance ministar muhalli ta Tarayyar Nijeriya inda ta jagoranci kokarin kasar kan ayyukan sauyin yanayi da kokarin kare muhalli.

Ms. Mohammed ta fara shiga Majalisar Dinkin Duniya ne a shekarar 2012 a matsayin mai baiwa Ban Ki-moon tsohon babban sakataren Manofofin Ci Gaban Karni Na Majalisar Dinki Duniya (MDD) shawara Ta musamman da alhakin tsare-tsaren ci gaba bayan 2015.

Ta jagoranci tsarin da ya haifar da yarjejeniyar duniya ta shirin cigaba mai dorewa Nan da 2030.

Labarai Masu Nasaba

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Ms. Mohammed ta fara aikinta ne da aikin zayyana makarantu da asibitoci a Nijeriya. Ta yi aiki a matsayin mai ba da shawara ta mayar da hankali kan inganta ilimi da sauran ayyukan zamantakewa, kafin ta shiga cikin ma’aikatun gwamnati, inda ta kai matsayin mai ba da shawara ga shugabannin hudu da suka biyo baya a kan talauci, gyara sassan gwamnati, da ci gaba mai dorewa.

An bai wa Ms. Mohammed digirin girmamawa da dama, kuma ta yi aiki a matsayin mataimakiyar farfesa, inda ta yi lacca kan ci gaban kasa da kasa. Wadda ta samu lambobin yabo daban-daban na duniya, Ms. Mohammed ta yi aiki a manyan kwamitocin ba da shawarwari na kasa da kasa. Tana da ‘ya’ya shida kuma tana da jikoki hudu.

MADOGARA (UN ORGANIZATION)

Haihuwa

An haifi Amina Jane Mohammed a Birnin Liberpool, dake Ingila a ranar 27 ga watan Yunin, 1961 mahaifinta likitan dabbobi ne  da kuma mahaifiyarta malamar Jinya ce (nurse) Asalin ta Bafulatana ce  daga Jihar Gombe Nijeriya.

Karatu

Amina ta halarci makarantar firamare a Kaduna da birnin Maiduguri a Nijeriya, sai kumaMakarantar “The Buchan School” da ke tsibirin Isle of Man.

Daga bisani ta halarci kwalejin Henley Management College dake birnin London a 1989. Bayan ta kammala karatun ta ne mahaifinta ya nemi ta da ta dawo gida Nijeriya.

Ayyuka

A tsakanin shekarun 1981 zuwa 1991, Amina tayi aiki da “Archcon Nigeria”, wani kamfanin zane-zane da suke da alaka da kamfanin zane-zane na Norman and Dawbarn da ke Ingila A 1991, ta samar da kamfanin Afri-Projects Consortium, sannan daga 1991 zuwa 2001 itace darekta mai zartarwa na kamfanin.

Daga shekara ta 2002 har zuwa shekara ta 2005, Amina ta shirya wani gangami da ilimantarwa game da jinsi karkashin United Nations Millennium Project. (Manufar manufar ita ce rage talauci, yunwa, cututtuka, jahilci, gurbacewar muhalli, da kuma cin zarafi tsakanin jinsi)

Amina ta rike matsayin mataimakiya ta musamman (Senior Special Assistant) na shugaban kasa akan shirin Millennium Debelopment Goals, Manofofin Cigaban Karni Na Majalisar Dinki Duniya (MDGs). A cikin shekara ta 2005, an zarge ta da amfani da kudin tallafi na kasa a wajen ayyukan MDGs.

Amina ta kasance wacce ta kafa kuma ta samar da kamfanin Center for Debelopment Policy Solution, sannan kuma a matsayin farfesa ta daliban masters a jami’ar Columbia.

A tsakanin wannan lokaci, tayi aiki a matsayin mai bada shawarwari na kungiyoyi daban daban na duniya wanda ya hada da, babban sakatariya a Majalisar Dinkin Duniya (UN) don zama na musamman akan Post-2015 “Debelopment Agenda”; da kuma Independent Edpert Adbisory Group.

Sannan har wayau ta rike matsayin chairman a Hukumar Ilimi, Kimiyya da Al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya United Nations Educational, Scientific and Cultural Organization (UNESCO), da sashin bincike da bayanai akan ilimi na duniya “Global Monitoring Report on Education” (GME).

Har zuwa shekara ta 2012, Amina tana daya daga cikin muhimman mutane a taron e Post-2015 Debelopment Agenda, (Ajandar ci gaban bayan 2015 wani tsari ne daga 2012 zuwa 2015 wanda Majalisar Dinkin Duniya ke jagoranta don ayyana tsarin ci gaban duniya nan gaba wanda zai cimma nasarar muradun karni, Sabon tsarin, wanda ya fara daga 2016 ana kiransa Manufofin Ci Gaban Dorewa). inda take aiki a matsayin mai bada shawara na musamman ga shugaban majalisar dinkin duniya watau Ban Ki-moon, sannan tana daga cikin mutane na musamman na “High Lebel Panel of Eminent Persons (HLP)” da majalisar Open Working Group (OWG) da dai sauransu.

Daga shekara ta 2014, tayi aiki a matsayin babban sakatariya na “independent Edpert Adbisory Group on the Data Rebolution for Sustainable Debelopment.

Ministan Muhalli (2015-2017)

Amina tayi aiki a matsayin ministan muhalli a karkashin mulkin shugaba Muhammadu Buhari daga watan Nuwamaban shekara ta 2015 zuwa watan Febrerun shekara ta 2017. A wannan lokaci itace wakiliyar Nijeriya a Kungiyar Kasashen Nahiyar Afurka wato “African Union (AU)” fannin kawo canji wanda Paul Kagame ke jagoranta.

Ta ajiye aikin Ministan muhalli a ranar 24 ga watan Febrerun 2017.

A cikin shekara ta 2017, wata kungiya mai zaman kanta ta zargi Amina da cewa tana ba da izini ga kamfanonin kasar China wajen diban itace timber zuwa kasashensu ba tare da izinin gwamnatin tarayya ba, a lokacin tana ministan muhalli na Nijeriya.

Amma daga bisani gwamnatin Nijeriya ta karyata zargin.

Mun samo daga Turakar Saliadeen a Dandalin Is’haki Idris Guibi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Amina MuhammadTarihi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Za Ta Daina Ciyar Da Fursunoni Abinci

Next Post

Xi Ya Yi Kira Da A Mayar Da Yankin Biranen Beijing Da Tianjin Da Hebei Mafarin Neman Zamanantar Da Kasar Sin

Related

tusar gaba
Adon Gari

Ko Kin San… Dalilin Da Ke Sa Mata Ke Ganin Farin Ruwa Kafin Ko Bayan Al’adarsu?

2 weeks ago
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

1 month ago
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
Adon Gari

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

2 months ago
Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

4 months ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

4 months ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

7 months ago
Next Post
Xi Ya Yi Kira Da A Mayar Da Yankin Biranen Beijing Da Tianjin Da Hebei Mafarin Neman Zamanantar Da Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Mayar Da Yankin Biranen Beijing Da Tianjin Da Hebei Mafarin Neman Zamanantar Da Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

September 15, 2025
Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

September 15, 2025
Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

September 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.