Babban mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro (NSA), Nuhu Ribadu, ya kara jaddada gargadinsa kan ci gaba da biyan kudaden fansa ga masu garkuwa da mutane, duk da wasu na ganin hakan a matsayin sauki garesu amma illa ne sosai.
Ribadu ya yi gargadin ne a lokacin da ya amshi sabbin mutane 60 da aka sako daga hannun masu garkuwan, biyo bayan azama da sojoji suka sanya a Jihar Kaduna.
- Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya
- Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga cikin wadanda aka sako har da mataimakin daraktan a ma’aikatar gwamanti da kuma dan uwan Bishop Matthew Hassan Kukah, wadanda dukkanin suka fito daga Zango Kataf da ke kudancin Kaduna.
A cewar Ribadu, biyan kudin fansa shi ke kara rura wutar garkuwa da mutane kuma shi ne ke kara wa masu garkuwan karfi, don haka daina ba su zai taimaka wajen rage musu satar mutane.
“Bari na roki mutanenmu, iyalai da su daina bai wa ‘yan ta’adda kudade. Don Allah a daina ba su kudade. Kudin da kuke ba su na kara rura matsalar. Ba mu taba bai wa wadannan mutane kudin. Bai wa wadanda sheidanun kudade shi ne ke kara ba su damar satar wasu a gaba. Yawan kudin da kuke ba su, yawan kara neman kudin da suke yi,” ya shaida.
Wani rahoton tsaro da hukumar Kididdiga (NBS) ta fitar a watan Disamban 2024, ta ce, yawan kudin fansa da jama’an Nijeriya suka biya ya zarce naira tiriliyan 2.23 ga masu garkuwa da mutane daga Mayun 2023 zuwa Afrilun 2024.
A cewar rahoton na CESPS, kusan kashi 65 cikin 100 na magidanta da suka fuskanci matsalar sace-sacen jama’a sun biya matsakaitan kudin fansa na naira miliyan 2.67, wanda ya kai naira tiriliyan 2.23.
An fitar da rahoton ne kwana guda bayan rahoton hukumar kare kakkin Dan’adam na Nijeriya na shekarar 2024, ya nuna cewa akalla mutane 526 ne aka kashe a wasu munanan hare-hare tare da yin garkuwa da wasu 949 a wasu sassan kasar.
Duk da masana sun sha nusar da jama’a illar biyan kudaden fansa ga ‘yan fashin daji, mutane ko iyalai suna ganin biyan kudin shi ne mafita a garesu a duk lokacin da aka sace musu wani nasu, lamarin da ke kara nuna sakacin jami’an tsaro, a cewar mutane da dama in ba su biya kudin fansar ba suna iya rasa dan uwan nasu da aka sace.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp