Mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara kan harkar tsaro, Nuhu Ribadu, ya buƙaci ‘yan Nijeriya da su daina biyan ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane kuɗin fansa, inda ya ce hakan na ƙara dagula lamarin tsaro a ƙasar nan.
Ribadu ya faɗi haka ne a Abuja ranar Talata yayin da yake karɓar mutum 64 da dakarun tsaro suka ceto daga hannun masu garkuwa da mutane a Kudancin Kaduna.
- Gwamna Zulum Ya Yi Allah-wadai Da Sabbin Hare-haren Boko Haram Da Sace-sacen Mutane A Borno
- ‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Satar Mota A Bauchi
Ya bayyana cewa biyan kuɗin fansa ba shi ne ke kuɓutar da mutane ba, domin yawanci bayan an biya kuɗin, ba a sakin waɗanda aka sace.
“Iyalai da dama sun biya kuɗin fansa amma hakan bai sa an sako ‘yan uwansu ba. Sojoji da jami’an tsaro ne suke ceto su ba tare da an biya ko sisi ba,” in ji Ribadu.
Ya yaba wa dakarun soji da sauran jami’an tsaro bisa jajircewarsu, tare da gode wa Shugaba Bola Tinubu bisa goyon bayan da yake bai wa ɓangaren tsaro.
Daga cikin mutanen da aka ceto akwai babban jami’i a ma’aikatar gwamnati da kuma wani ɗan uwa ga Bishop Matthew Hassan Kukah.
An ruwaito cewa sun kwashe fiye da wata guda a hannun waɗanda suka sace su.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp