ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Ƙabilanci Da Saɓanin Makiyaya Da Manoma Ya Zama Tarihi A Jihar Kaduna – KSPC

by Sulaiman and Shehu Yahaya
11 months ago
Kaduna

Hukumar wanzar da zaman lafiya ta Jihar Kaduna ( Kaduna State Peace Commission ) Ta bayyana cewa, matsalar rikice-rikicen Ƙabilanci da na Fulani Makiyaya da Manoma yanzu ya zama tarihi a faɗin jihar baki ɗaya.

 

Muƙaddashiyar Mataimakiyar Shugabar Hukumar, Hajiya Khadija Hawaja Gambo ce ta tabbatar da hakan yayin taron bita akan ayyukan hukumar na shekaru biyar da suka gabata tare da wasu kungiyoyin wanzar da zaman lafiya a jihar Kaduna,  wanda ya gudana a ɗakin taro na gidan Hassan Usman Katsina da ke Kaduna.

ADVERTISEMENT
  • Sin A Shirye Take Ta Shawo Kan Sabani Tare Da Sabuwar Gwamnatin Amurka
  • Jami’o’in Sin Da Najeriya Sun Yi Kira Da A Yaukaka Fahimta Tsakanin Al’adun Kasashe Masu Tasowa

Hajiya Gambo, ta ce “Yau fiye da Shekaru Biyar ba a samu matsalar ɓarkewar rikice-rikicen kabilanci ko Fulani makiyaya da manoma ba, wanda hakan ya furu ne bisa jajircewar hukumarmu wajen samun haɗin kan ɗaukacin al’ummar jihar Kaduna.

 

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

“Nasan yanzu an manta shekarar da aka samu rikicin kabilanci ko Fulani makiyaya da manoma a kaduna kuma idan babu hadin kan mutane, ba za mu samu wannan nasarar ba, wannan yana nuna cewa kowa yana da rawar takawa, ba wai kawai nauyi ne da ya rataya akan hukumarmu ba har da ma hada hannu da shugabannin al’umma da masu ruwa da tsaki wajen samar da tsare-tsaren wanzar da zaman lafiya. Muna aiki ba dare ba rana don neman zaman lafiya ya dore acikin al’ummar jiharmu”.

 

“Don haka, a yanzu Kaduna duk wani rikicin kabilanci ya zama tarihi, muna fata, jihar Kaduna ta zama abin koyi ga sauran jihohin da ke fama da irin wannan matsalar, su samu ilimin yadda muka yi muka warware namu matsalar, saboda haka, mu kullum a shirye muke wajen tabbatar da cewa an samu hadin kai da zaman lafiya a tsakanin al’ummarmu baki daya”.

 

A nata jawabin, babbar Daraktar kungiyar wayar da kan mata ta jihar Kaduna, Misis Hannatu Aruwan, ta bayyana gamsuwarta dangane da matakan da hukumar wanzar da zaman lafiya ta jihar Kadauna ke aiwatarwa wajen kara hada kan daukacin alummar jihar.

 

Akan hakan, Hannatu Aruwan ta bukaci gwamnatin jihar Kaduna da ta kara tallafa wa hukumar da kudade wajen ci gaba da kokarinta na wanzar da zaman lafiya da hadin kan al’umma wajen warware duk wata matsala da ke barazana ga wanzar da zaman lafiya a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

December 22, 2025
An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Next Post
Nijeriya Ta Yaba wa Yarjejeniyar Tsagaita Wuta a Gaza

Nijeriya Ta Yaba wa Yarjejeniyar Tsagaita Wuta a Gaza

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

December 22, 2025
An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.