• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Ƙabilanci Da Saɓanin Makiyaya Da Manoma Ya Zama Tarihi A Jihar Kaduna – KSPC

by Sulaiman and Shehu Yahaya
8 months ago
in Labarai
0
Rikicin Ƙabilanci Da Saɓanin Makiyaya Da Manoma Ya Zama Tarihi A Jihar Kaduna – KSPC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar wanzar da zaman lafiya ta Jihar Kaduna ( Kaduna State Peace Commission ) Ta bayyana cewa, matsalar rikice-rikicen Ƙabilanci da na Fulani Makiyaya da Manoma yanzu ya zama tarihi a faɗin jihar baki ɗaya.

 

Muƙaddashiyar Mataimakiyar Shugabar Hukumar, Hajiya Khadija Hawaja Gambo ce ta tabbatar da hakan yayin taron bita akan ayyukan hukumar na shekaru biyar da suka gabata tare da wasu kungiyoyin wanzar da zaman lafiya a jihar Kaduna,  wanda ya gudana a ɗakin taro na gidan Hassan Usman Katsina da ke Kaduna.

  • Sin A Shirye Take Ta Shawo Kan Sabani Tare Da Sabuwar Gwamnatin Amurka
  • Jami’o’in Sin Da Najeriya Sun Yi Kira Da A Yaukaka Fahimta Tsakanin Al’adun Kasashe Masu Tasowa

Hajiya Gambo, ta ce “Yau fiye da Shekaru Biyar ba a samu matsalar ɓarkewar rikice-rikicen kabilanci ko Fulani makiyaya da manoma ba, wanda hakan ya furu ne bisa jajircewar hukumarmu wajen samun haɗin kan ɗaukacin al’ummar jihar Kaduna.

 

Labarai Masu Nasaba

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

“Nasan yanzu an manta shekarar da aka samu rikicin kabilanci ko Fulani makiyaya da manoma a kaduna kuma idan babu hadin kan mutane, ba za mu samu wannan nasarar ba, wannan yana nuna cewa kowa yana da rawar takawa, ba wai kawai nauyi ne da ya rataya akan hukumarmu ba har da ma hada hannu da shugabannin al’umma da masu ruwa da tsaki wajen samar da tsare-tsaren wanzar da zaman lafiya. Muna aiki ba dare ba rana don neman zaman lafiya ya dore acikin al’ummar jiharmu”.

 

“Don haka, a yanzu Kaduna duk wani rikicin kabilanci ya zama tarihi, muna fata, jihar Kaduna ta zama abin koyi ga sauran jihohin da ke fama da irin wannan matsalar, su samu ilimin yadda muka yi muka warware namu matsalar, saboda haka, mu kullum a shirye muke wajen tabbatar da cewa an samu hadin kai da zaman lafiya a tsakanin al’ummarmu baki daya”.

 

A nata jawabin, babbar Daraktar kungiyar wayar da kan mata ta jihar Kaduna, Misis Hannatu Aruwan, ta bayyana gamsuwarta dangane da matakan da hukumar wanzar da zaman lafiya ta jihar Kadauna ke aiwatarwa wajen kara hada kan daukacin alummar jihar.

 

Akan hakan, Hannatu Aruwan ta bukaci gwamnatin jihar Kaduna da ta kara tallafa wa hukumar da kudade wajen ci gaba da kokarinta na wanzar da zaman lafiya da hadin kan al’umma wajen warware duk wata matsala da ke barazana ga wanzar da zaman lafiya a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Samun Ingantar Tattalin Arziki

Next Post

Nijeriya Ta Yaba wa Yarjejeniyar Tsagaita Wuta a Gaza

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

49 minutes ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

2 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya
Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

3 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

4 hours ago
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

16 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

16 hours ago
Next Post
Nijeriya Ta Yaba wa Yarjejeniyar Tsagaita Wuta a Gaza

Nijeriya Ta Yaba wa Yarjejeniyar Tsagaita Wuta a Gaza

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.