• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Bayan Zabe: Bamu Amince Da Sakamakon Zaben Sanata A Adamawa Ba – ‘Yan Takara 5

by Muh'd Shafi'u Saleh
3 years ago
in Siyasa
0
Rikicin Bayan Zabe: Bamu Amince Da Sakamakon Zaben Sanata A Adamawa Ba – ‘Yan Takara 5
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bisa zargin aikata ba daidai ba, lokacin gudanar da zaben kujerar dan majalisar dattawa mai wakiltar Adamawa ta kudu, ‘yan takara 5, sunki amincewa da sakamamon zaben fidda gwanin bisa zargin ba’abi ka’ida ba.

‘Yan takaran biyar, sun roki kwamitin gudanar da zaben da ta sanar da Adamu Isma’ila Numun da cewa ya lashe zaben, da ta soke takaransa, bisa cewa ya karya dokar zabe, da sayen kuri’u, don haka bai cancanci tsayawa takaran ba.

  • Kama Ta Ya Yi APC Ta Fitar Da Dan Takarar Shugaban Kasa Daga Kudu —Sanata Gaya

Da su ke magana da ‘yan jaridu a Yola, ‘yan takaran Baresta Bala Sanga, Bridget Zidon, Grace Bent, Sani Jada, Ahmad Abubakar, sun tabbatar da cewa basu shiga zaben da’akace Adamu Isma’ila ya lashe zaben ba.

Da yake magana amadadin ‘yan takaran Baresta Sanga yace “bukatarmu shine su yi amfani da takardar da muka basu ranar 29 ga Mayu 2022, cewa Adamu Isma’ila Numun, bai cancanci takara ba, saboda sayen kuri’un da yayi, lokacin zabe.

“Wannan abin kunya ne ga jam’iyya, a kafa wani kwamitin da zai gudanar da sabon zabe, kuma a canja wurin gudanar da zaben, daga Numan zuwa inda ya dace a yankin.

Labarai Masu Nasaba

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

“Mun gaskata jam’iyyar APC zata gudanar mana da adalci, duk da ba’a da kaskancin da Adamu Isma’ila Numan, ya shigo dashi, bamu cire tsammani ga bukatunmu ba, muna zaman jiran mu bayyana gaban kwamitin amsar koke” inji Sanga.

‘Yan takaran sun kuma bayyana cewa ba’ayi zaben fidda gwani a yankin ba, ya kamata a gudanar da zaben a ranar 29 ga Mayu 2022, duk mu bama wurin, mu munyi imanin an tsara ne da raba mana kuri’un.

“Mafiya yawan masu zabenmu sun koma garuruwansu, kuma gurare ne mai nisa, kusan mutum zaiyi awa 4, abune da ba zai yiwu ba ka taro duka masu zabe, duk da babu masu zabemmu da masu sa mana ido, a zahiri ci gaba da zabe a haka abin kunya ne.

“A irin wannan zaben fidda gwanin da takardar kada kuri’a, da duk ‘yan takara, da masu sa ido, za su amince, mu ‘yan takara da masu sa mana ido bamu a wurin zabe, sunyi abinda ya musu ne kawai.

“Muna bukatar kwamitin sauraren koke-koken zabe ta lura da wadannan manyan batutuwa wadanda suke nuna makurar rashin adalci, an tura mana sako karfe 8:54 na safe cewa za’ayi zaben 12 na rana.

“Kawai awanni uku da mintuna 6 aka bamu, mu shirya a yi zaben fidda gwanin, yaushe zamu tattaro kan masu zabenmu? Wannan wani irin makoran rashin adalci ne” inji Sanga.

Da yake maida kalami kan zargin da ‘yan takaran sukayi Adamu Isma’ila Numan, yace “kawai don basu sukayi nasara bane, dabi’ace ta wanda ya fadi zabe

“Tunda farko mun yarda masu sa mana ido, su taimakawa wadanda basu iya rubutu ba, lokacin da mai sa mini ido zai taimaki mai zabena, suka fara cewa sayen kuri’u sayen kuri’u.

“Ni bansan komai akan haka ba, ni ban umurci wani ko wasu su dauki doka a hannu amadadina ba, amma aka dakatar da zaben.

“Lokacin da’aka sanar za’ayi zabe, na nemo masu sa mini ido da masu zabe, mun tafi wurin zabe mukayi zabe kuma munci zaben” inji Numun.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Zambia Ta Kaddamar Da Dakin Taro Na Zamani Da Sin Ta Gina A Kasar

Next Post

Yadda Aka Yi Wa Wata Mata Yankan Rago A Hadejia

Related

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
Siyasa

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

2 days ago
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
Siyasa

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

3 days ago
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Siyasa

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

3 days ago
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

4 days ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

1 week ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

1 week ago
Next Post
Yadda Aka Yi Wa Wata Mata Yankan Rago A Hadejia

Yadda Aka Yi Wa Wata Mata Yankan Rago A Hadejia

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.