• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Cikin Gida: Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano Ta Kama Ɗan Bindiga Da Ya Tsere Wa ‘Yan’uwansa

by Sulaiman
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Rikicin Cikin Gida: Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano Ta Kama Ɗan Bindiga Da Ya Tsere Wa ‘Yan’uwansa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan jihar Kano ta kama wani dan bindiga mai suna Isah Lawal mai shekaru 33 da ya baro yankin Birnin Gwari da ke jihar Kaduna.

Lawal wanda ya kware a harkar fashi da makami, garkuwa da mutane, da satar shanu, an kama shi ne a wani samame da jami’an ‘yansanda karkashin jagorancin SP Aliyu Mohammed Auwal suka gudanar a jihar Kano a wani rahoton sirri da suka samu.

  • Cire Tallafin Fetur: Ma’aikatan Jihar Jigawa Sun Ki Amincewa Da Karin Albashin Naira 10,000
  • An Gudanar Da Bukukuwan Shagalin Murnar Bikin Bazara Na CMG A Habasha Da Amurka Da Rasha

A ranar 4 ga watan Janairun shekarar 2024 ne aka kai samamen a karamar hukumar Karaye ta jihar da ke kan iyakar Kaduna da Kano, inda aka kwato shanu 55 da tumaki shida.

Dan bindigan Wanda ake zargin mazaunin kauyen Kaya ne da ke karamar hukumar Giwa a jihar Kaduna, ya amsa cewa, ya tsere ne daga sansaninsu na ‘yan bindigar Maidaro da ke karamar hukumar Birnin Gwari sakamakon rikicin cikin gida da ya kaure tsakanin ‘yan sansanin.

Bayanin da Lawal ya yi a lokacin binciken, ya nuna cewa, ya koma jihar Kano musamman dajin Gwarzo-Karaye ne sakamakon mutuwar daya daga cikin shugabannin kungiyar, Bashir na Malumfashi a jihar Katsina, a yayin artabu da wata kungiyar ‘yan bindiga da ke hamayya da juna.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

Mataimakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan (DPPRO), ASP Abdullahi Hussaini, a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai, inda ya tabbatar da kama wannan dan ta’addan, ya yaba da kokarin jami’an ‘yansandan, ya kuma bayyana cewa, kwamishinan ‘yansandan, CP Mohammed Usaini Gumel, ya umurci a kara yawan jami’an ‘yan sandan da ke aiki kan iyakokin jihar don kare dukkan iyakokin jihar Kano.

CP Gumel ya nuna jin dadinsa da irin goyon baya da hadin kai da jama’ar jihar suka ba su, inda ya bukaci a ci gaba da sanya ido tare da kai rahoton duk wani abu da ake zargi ga ofishin ‘yansanda mafi kusa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dazukan Katsina da ZamfaraSatar ShanuTa'addancin 'yan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kun Kasa Magana A Lokacin Buhari, Ba Ku Da Damar Sukar Tinubu – Matasan Arewa

Next Post

Shugaban Karamar Hukuma A Kano Ya Yi Murabus, Wani Kuma Ya Fice Daga APC Zuwa NNPP

Related

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

2 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

4 hours ago
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Manyan Labarai

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

8 hours ago
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

12 hours ago
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

15 hours ago
Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

1 day ago
Next Post
Shugaban Karamar Hukuma A Kano Ya Yi Murabus, Wani Kuma Ya Fice Daga APC Zuwa NNPP

Shugaban Karamar Hukuma A Kano Ya Yi Murabus, Wani Kuma Ya Fice Daga APC Zuwa NNPP

LABARAI MASU NASABA

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

June 4, 2025
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.